Home Labarai Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty international tayi Allah wadai da abin da ta kira tauye hakkin dan adam da rundunar ‘yan sanda Nijeriya ke ci gaba da yiwa tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da karbar korafe korafe ta jihar Kano Muhuyi magaji Rimin Gado.

Ta cikin wani sautin murya da shugaban hukumar gudanarwa ta kungiyar ya aikewa PRNigeria Hausa, ya bayyana cewa kungiyar ta yi tofin alatsine kan yadda ake ci gaba da musgunawa gami da tauyi hakkin Muhuyi duk dace doka bata bawa ‘yan sandan damar kama shi ba, haka kuma babu wata kotu da ta bada umarnin yin kamun.

Kungiyar ta bukaci rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta gaggauata sakin Muhuyi tare kuma da daina cin zarafinsa da sauran Al’ummar Nijeriya.

Ba dai wannan ne karon barko da dakarun ‘yan sandan ke yiwa Muhuyi wannan kamu ba, duk da cewa ana kallon hakan na da nasaba da takun saka da yake fuskanta da wasu ‘yan siyasa a jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp