Home Labarai Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty international tayi Allah wadai da abin da ta kira tauye hakkin dan adam da rundunar ‘yan sanda Nijeriya ke ci gaba da yiwa tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da karbar korafe korafe ta jihar Kano Muhuyi magaji Rimin Gado.

Ta cikin wani sautin murya da shugaban hukumar gudanarwa ta kungiyar ya aikewa PRNigeria Hausa, ya bayyana cewa kungiyar ta yi tofin alatsine kan yadda ake ci gaba da musgunawa gami da tauyi hakkin Muhuyi duk dace doka bata bawa ‘yan sandan damar kama shi ba, haka kuma babu wata kotu da ta bada umarnin yin kamun.

Kungiyar ta bukaci rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta gaggauata sakin Muhuyi tare kuma da daina cin zarafinsa da sauran Al’ummar Nijeriya.

Ba dai wannan ne karon barko da dakarun ‘yan sandan ke yiwa Muhuyi wannan kamu ba, duk da cewa ana kallon hakan na da nasaba da takun saka da yake fuskanta da wasu ‘yan siyasa a jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp