Home Labarai ICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRA

ICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRA

Hukumar yaƙi da almundahana ta Najeriya ICPC ta ce za ta yi bincike kan zargin da shugaban rukunin kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya yi wa shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, Ahmed Farouk.

Dangote ya mika ƙorafi ga hukumar ICPC a ranar Talata, inda ya zargi Farouk da cin hanci da rashawa da almundahanar kuɗaɗen gwamnati.

Bayan sa’o’i kaɗan da shigar da ƙorafin, ICPC ta tabbatar da karɓarsa tare da bayyana aniyarta ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, John Odey, ya fitar a shafukan sada zumunta na ICPC, ya ce “Hukumar ta karɓi ƙorafin Dangote a hukumance a ranar Talata 16 ga Disamba, 2025, ta hannun lauyansa.”

A cikin ƙorafin, “Dangote ya zargi Farouk da kashe sama da dala miliyan 7 wajen biyan kuɗin karatun ’ya’yansa huɗu a makarantu a ƙasar Switzerland na tsawon shekaru shida, ba tare da bayyana sahihiyar hanyar samun kuɗin ba.

Korafin ya ce Farouk ya yi amfani da muƙaminsa a NMDPRA wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati domin amfanin kansa, lamarin da ya janyo asara ga ’yan Najeriya.

A nasa martanin, shugaban hukumar NMDPRA, Ahmed Farouk, ya ce yana maraba da binciken da hukumar ICPC za ta gudanarwa a kansa.

Ya ce ya yi imanin cewa binciken zai ba da dama a duba lamarin cikin adalci da natsuwa, tare da fayyace gaskiyar al’amura domin wanke sunansa.

Ahmed Farouk ya ƙara da cewa ba zai yi musayar zarge-zarge a bainar jama’a ba yana mai cewa zai bari binciken hukuma ya yi aikinsa yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp