ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da bincike kan tsohon shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, (NMDPRA), Farouk Ahmed, duk da cewa attajiri mafi kuɗi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote ya janye ƙorafin da ya shigar a kansa.

Lauyan Dangote, Ogwu Onoja, ne ya aika takardar janye ƙorafin zuwa ga ICPC.

Dangote dai ya buƙaci hukumar ta binciki Ahmed a watan Disamban 2025 kan zargin amfani da muƙaminsa wajen satar kuɗaɗen gwamnati, inda ya ce yana da hujjoji da suka tabbatar da zarginsa.

Sai dai, mai magana da yawun ICPC, John Odey, ya bayyana cewa duk da janyewar ƙorafin, hukumar za ta ci gaba da bincike domin tabbatar da gaskiya da adalci da kuma yaƙi da cin hanci a Najeriya.

Odey ya ƙara da cewa ci gaba da binciken zai nuna cewa hukumar na yin aikinta ba tare da la’akari da matsayi ko shaharar mutum ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com