Home Labarai ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote...

ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da bincike kan tsohon shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, (NMDPRA), Farouk Ahmed, duk da cewa attajiri mafi kuɗi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote ya janye ƙorafin da ya shigar a kansa.

Lauyan Dangote, Ogwu Onoja, ne ya aika takardar janye ƙorafin zuwa ga ICPC.

Dangote dai ya buƙaci hukumar ta binciki Ahmed a watan Disamban 2025 kan zargin amfani da muƙaminsa wajen satar kuɗaɗen gwamnati, inda ya ce yana da hujjoji da suka tabbatar da zarginsa.

Sai dai, mai magana da yawun ICPC, John Odey, ya bayyana cewa duk da janyewar ƙorafin, hukumar za ta ci gaba da bincike domin tabbatar da gaskiya da adalci da kuma yaƙi da cin hanci a Najeriya.

Odey ya ƙara da cewa ci gaba da binciken zai nuna cewa hukumar na yin aikinta ba tare da la’akari da matsayi ko shaharar mutum ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp