Home Labarai Kwankwaso ya zargi yadda ake matsawa wasu shuwagabannin kananan hukumomi a jihar...

Kwankwaso ya zargi yadda ake matsawa wasu shuwagabannin kananan hukumomi a jihar Kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya zargi yadda yace ana matsa wa wasu shugabannin ƙananan hukumomi lamba domin su fice daga tsarin Kwankwasiyya.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a yau Talata, cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

In da ya ce ya samu kiraye-kiraye daga wasu shugabannin ƙananan hukumomi da kuma ’yan Majalisar Jiha, inda ake buƙatar su sanya hannu domin komawa jam’iyyar APC.

Ya ƙara da cewa yana ƙarfafa gwiwar masu ci gaba da kasancewa cikin tsarin Kwankwasiyya, tare da ba su tabbacin cewa za su yi aiki tare domin fuskantar zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

Daga bisani Kwankwaso ya yabawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya yabi Gwamnatinsa ya kuma kushe gwamnatin da ta gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp