Ƴanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 160 a coci a Kaduna

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

A jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, rahotanni sun nuna cewa wasu ƴanbindiga sun yi garkuwa da sama da mutane 160 a wasu coci-coci da ke ƙauyen Kurmin Wali a ƙaramar hukumar Kajuru a jihar. Lamarin dai ya auku ne ranar Lahadi, lokacin da mutanen ke ibada a coci da ke ƙauyen.

Shi ma shugaban ƙungiyar kiristoci ta Najeriya CAN, reshen jihar Kaduna Reberan Joseph John Hayab ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar Daily Trust.

Ya ce, “duk da cewa ban cika son ambata adadi ba, amma bayanan da na samu daga yankin na nuna cewa ƴanbindiga sun sace kusan mutum 172, amma guda 9 sun tsere sun koma gida, amma har yanzu ana neman mutum 163,” in ji shi.

Ya ce ko ma dai mene ne maƙasudin sace mutanen, “ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba. Za mu ci gaba da ba jami’an tsaro da gwamnati haɗin kai domin tabbatar da ceto mutanen.”

Har zuwa lokacin haɗa wannan labarin dai gwamnatin jihar Kaduna da rundunar ƴansandan jihar ba su ce komai ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com