Home Labarai Abba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano –...

Abba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano – Dawakin Tofa

Gwamnatin jihar Kano ta fitar da wata sanarwa domin yin ƙarin haske kan ganawar da gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya yi da shugaban Najeriya Bola Tinubu.

A yammacin Litinin ne gwamnan, wanda aka daɗe ana raɗe-raɗin komawarsa jam’iyyar APC mai mulki daga jam’iyyar NNPP ya gana da Bola Tinubu, inda ake sa ran cewa tattaunawar ta ƙunshi batun cimma yarjejeniya kan sauya sheƙar gwamnan.

Sai dai a sanarwar da gwamnatin ta fitar ta hannun mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature, ta ce gwamnan da shugaban ƙasa sun tattauna ne kan muhimman abubuwa da suka shafi tsaro da samar da ayyukan more rayuwa.

Sanarwar ta ce ganawar, wadda aka yi a asirce, “ta bai wa gwamnan damar yi wa shugaban ƙasa bayani kan manyan ƙalubale da jihar Kano ke fuskanta musamman taɓarɓarewar tsaro a wasu ƙananan hukumomi.

“Gwamna Yusuf ya kuma yi wa shugaban ƙarin bayani kan matar da aka kashe da ’ya’yanta shida kwanan nan, yana mai jaddada buƙatar gaggawar tallafin gwamnatin tarayya domin ƙarfafa ayyukan tsaro da kare rayukan fararen hula.

“Ya kuma bayyana rawar da Rundunar Tsaro ta Jihar Kano ke takawa wajen taimaka wa hukumomin tsaro, tare da neman ƙarin haɗin gwiwa da hukumomin tsaron tarayya.

“A ɓangaren raya ƙasa, gwamnan ya tattauna manufar ci gaban Kano, inda ya mayar da hankali kan manyan ayyukan gine-gine.

“A nasa ɓangaren, Shugaba Tinubu ya tabbatar wa gwamnan cewa “gwamnatin tarayya a shirye take ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Kano domin shawo kan matsalolin tsaro da kuma tabbatar da ci gaba mai ɗorewa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp