Home Labarai JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Haɗakar ƙungiyoyin ma’aikatan lafiya ta Najeriya, (JOHESU) ta ce ‘yan Najeriya su ɗora wa gwamnatin tarayya alhakin wahalhalun da marasa lafiya da sauran masu buƙatar kulawar lafiya ke fuskanta sakamakon yajin aikin da mambobinta ke yi.

Ƙungiyar ta ce buƙatarta ɗaya tilo ita ce aiwatar da rahoton da ya shafi daidaita tsarin albashin ma’aikatan kiwon lafiya na CONHESS.

Sakataren JOHESU na ƙasar, Martin Egbanubi ne ya bayyana hakan ne a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

Ya ce duk da sanin tasirin yajin aikin a kan ƴanƙasa, bai kamata a ɗora musu laifi ba.

Ya ce, “Mun san irin tasirin da yajin aikin ke yi wa ‘yan Najeriya, amma bai kamata ‘yan ƙasa su ɗora mana laifi ba. Gwamnati ce ya kamata ta ɗauki alhaki, domin ita ce ke da haƙƙin yin abin da ya dace domin kauce wa irin wannan yajin aiki a nan gaba.”

Egbanubi ya ƙara da cewa JOHESU na fahimtar halin da marasa ƙarfi ke ciki, musamman waɗanda ba su da ƙarfin zuwa asibitoci masu zaman kansu, amma ya ce mambobin ƙungiyar ma suna shan wahala.

Saboda haka, ƙungiyar ta buƙaci masu kishin kasa su yi kira ga gwamnati ta gaggauta magance buƙatar domin dakatar da yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp