Gwamnatin Najeriya ta bakin kakakin ma’aikatar tsaronta ta tabbatar da isowar sojojin Amurka aƙalla 100 cikin ƙasar ta yammacin Afrika don taimaka mata a yaƙin da ta ke da ƴan ta’addar da ke kaiwa jama’a hare-hare.
Kakakin shalkwatar tsaron Najeriyar Manjo Janar Samaila Uba ya ce tabbas sojojin Amurkan sun shiga Najeriyar amma ba za su shiga fagen daga don yin yaƙi ba, face aikin horar da dakarun Najeriyar dabarun yaƙi da ƴan ta’addan.
Isowar sojojin Amurka na zuwa bayan tun farko Donald Trump ya zargi Najeriyar da gazawa wajen baiwa Kiristoci kariya daga hare-haren da ƴanta’addan da ya kira da Musulmai ke kaiwa a sassan ƙasar.
Read Also:
Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargin bayan da ta ce ƴan ta’addan na kashe dukkanin ɓangarorin Musulmai da kuma Kiristoci kuma dakarunta na aiki tuƙuru wajen yaƙi da su musamman a yankin arewa maso yammaci da kuma arewa maso gabas.
Amurkan ta kai hare-hare cikin watan Disamba kan yankunan da ta ce a nan ne mayaƙan IS suke a yankin na arewa maso yammacin Najeriyar kuma tun daga wancan lokaci bayanai ke cewa akwai sojojin na Washington da jiragen yaƙinta da ke shawagi a sassan Najeriyar don yaƙi da matsalolin tsaron.
Cikin kwanakin baya-bayan nan anga tarin jiragen yaƙin Amurka ɗauke da ko dai sojoji ko kuma makamai na isa sassan jihohin arewacin ƙasar kamar yadda bayanan bin diddigin da kafar Reuters ke yi suka bayyana.
Tun a farkon watan nan ma’aikatar tsaron Najeriyar ta ce tana tsammanin isowar ƙarin Sojin Amurka 200 zuwa ƙasar.
Najeriya mai yawan jama’a fiye da miliyan 240 na da rinjaye mabiyan addinin Islama ne a yankin arewaci yayinda mabiya addinin Kirista ke a yankin kudanci.










