Home Labarai Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

President-Muhammadu-Buhari

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba da umarnin cewa a gaggauta sakin tan 40,000 na kayan Abinci daga asusun ajiyar hatsi na Gwamnatin Tarayya, domin taimakawa marasa karfi a yayin gudanar da bukukuwan Easter da sallah.

Ministan Noma da Raya Karkara Muhammed Mahmoud ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai na Fadar Shugaban Kasa bayan wata ganawar sirri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar sa dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata.

Mahmood, yace Shugaba Buhari ya bashi umarnin raba kayayyakin ga Al’ummar Nijeriya, ya kuma bayyana cewa yana fatan rabon kayan abincin zai ragewa Al’umma radadin hauhawar farashin kayan masarufi.

Ya kara da cewa, ton dubu 12 daga cikin dubu 40 da aka amince dasu za’a baiwa ma’aikatar kula da jin kai da bala’oi da ci gaban jama’a ta tarayya domin rabawa ‘yan gudun hijira a fadin kasar nan.

Economic Confidential ta rawaito ministan na cewa za’a yi amfani da tsarin da aka bi a lokacin kullen Corona (covid-19) a shekarar 2020, wajen raba ton dubu 70 na kayan abinci a wasu jihohin ciki har da birnin tarayya Abuja.

“Idan dai zaku iya tunawa, lokacin kullen corona a kasar nan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin fidda hatsi domin rabawa masu karamin karfi a Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp