Home Labarai NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

Tsohon Shugaban Mulkin Soji Yakubu Gowon ya kaddamar da sabbin Gidajen Radiyo da Talabishin mallakin hukumar kula da Masu Yiwa Kasa Hidima ta NYSC.

Gidan Radiyon na NYSC mai mita 88.3 fm da kuma gidan TV dake ka channel 365 akan TSTV.

Kaddamar da tashoshin da ya gudana a harabar hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ta NYSC ya sami halartar tsohon shugaban Najeriya Janar Yakubu Gowon, Ministan Wasanni da Matasa Sunday Dare, Tsoffin Daraktocin Hukumar, masu rike da sarautun gargajiya da sauran manyan mutane a fadin Nijeriya.

A jawabin sa, Yakubu Gowon ya yaba da kokarin Janar Shu’aibu Ibrahim, wanda karkashin shugabancin sa ne wannan hukuma ta sami gagarumar nasarar kafa gidan Radiyo da Talabishin.

Tun bayan kafa wannan hukuma tsahon shekaru 49, ta ciga da yaye matasa masu nagarta wanda ke kai kasar ga tudun muntsira.

Da yake jawabi tun da fari Babban Daraktan Hukumar Janar Shu’aibu, ya bayyana cewa samar da kafafen yada labaran na Radiyo da talabishin na matsayin wani bangare na inganta ayyukan hidimar kasar.

Yace dukkan kafafen na NYSC Radio da NYSC TV Mambobin hukumar hidimar kasar ne za suke sarrafasu da kuma wasu cikin ma’aikatan hukumar; haka kuma masu hidimar kasa dake da Muradin samun ilimi a fannin na aikin yada labarai suma suna da dama a kafafen.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp