Home DUNIYA Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Gwamnatin Somalia na samun goyon baya kan fafutukar da ta ke na ganin an janye takunkumin da aka kakaba mata na hana shigar da makamai kasar, inda a baya bayan nan, Habasha ta bi sahun Uganda wajen goyon bayan janye matakin.

A cikin watan Nuwamba ake sa ran kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri’a kan sabunta takunkumin haramta saidawa Somalia makamai, wanda gwamnati ta ce, cire shi zai taimaka mata wajen yakar mayakan ‘yan ta’adda na Al Shebaab.

Goyon bayan da Habasha ta bai wa Somalia, ya zo ne bayan da a watan Yuli, gungun mayakan Al Shebaab suka kutsa cikin iyakarta, a lokacin da su ke gujewa hare-haren sojojin Somalia.

A halin yanzu, shekaru akalla 30 kenan aka shafe takunkuman hana shigar da makaman na aiki kan Somalia, wadanda shugaban kasar Hassan Sheikh Mohamud da Firaministan Habasha Abiy Ahmed suka ce lokaci ya yi da za a janye su, domin ba da damar kaddamar da cikakken yaki kan mayakan Al Shebaab.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp