Shugaban kasar Afirka ta Kudu yace sun Damuwa da yadda kasashen duniya suka kauda kansu daga fafutukar samun yancin Yammacin Sahara

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sake jaddada goyan bayan kasar sa ga Yammacin Sahara don ganin ta zama kasa mai cin gashin kan ta daga kasar Morocco.

Ramaphosa ya bayyana haka ne lokacin da ya karbi shugaban kungiyar Polisario dake fafutukar kafa kasar Yammacin Saharar, Brahim Ghali wanda ya ziyarce shi a Pretoria.

Shugaban kasar yace suna matukar damuwa da yadda kasashen duniya suka kauda kansu daga fafutukar samun yancin Yammacin Sahara wadda kasar Morocco ta yiwa kamun kazar kuku.

Ramaphosa yace su a Afirka ta Kudu sun fahimci muhimmancin wannan fafutuka ta samun yancin kan yankin, kuma suna bayyana goyan bayan su dari-bisa-dari wajen ganin an samu nasarar yancin yankin domin baiwa jama’ar yankin abinda suke bukata.

Shugaban ya danganta fafutukar ‘yancin Yammacin Sahara da na yaki da wariyar jinsin kasarsu ta Afirka ta Kudu tayi, inda ya bayyana su a matsayin halartattun yake yaken da suka zama wajibi.

Kungiyar Polisario na fafutukar samun ‘yanci kai tun daga shekarar 1976, abinda ya sa ta fada rikici da Morocco wadda ta mamaye ta tun bayan mulkin mallakar da Spain ta yiwa yankin tsakanin shekarar 1884 zuwa 1975.

Kungiyar Polisario tace akalla kasashe 80 sun amince da fafutukar su, amma kuma Morocco taki amincewa ta bata ‘yancin kai.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 27 minutes 51 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 9 minutes 16 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com