Home Labarai Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Babban Sufeton Ƴan Sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya ce bai saɓa umarnin kotu ba sakamakon ba shi da masaniya kan wani hukunci da kotun ta yanke da ya shafi mayar da wani ɗan sanda kan aikinsa.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar inda tace babban sufeton ya ce an sallami ɗan sandan tun a 1992, shekaru kaɗan bayan shi kansa sufeton ya shiga aikin ɗan sanda.

Ya bayyana cewa hukunci na ƙarshe wanda kotu ta yanke a 2011 zamanin wani sufeto ne daban.

Sai dai Usman Alkali Baba ya ce ya bayar da umarni ga kwamishinan ƴan sanda wanda ke kula da ɓangaren shari’a da ya gudanar da bincike kan wannan zargin domin duba matsayar kotu da kuma ba sufeton shawarar da ta dace ta shari’a domin ɗaukar mataki.

A ɗazu ne Babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta yanke wa Sufeton Ƴan sandan ƙasar hukuncin zaman gidan yari na wata uku.

Mai Shari’a Justice Mobolaji Olajuwon ce ta yanke hukuncin inda ta ce ya saɓa umarnin kotu kamar yadda kafar watsa labarai ta Channels a Najeriya ta ruwaito.

Tun farko dai wani ɗan sanda mai suna Patrick Okoli ne ya shigar da ƙara inda ya ce an yi masa ritaya ƙarfi da yaji a 1992 inda daga baya kotu ta bayar da umarnin a mayar da shi kan aikinsa tare da biyansa duka haƙƙoƙinsa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp