Home Labarai Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Sefeton ‘yan Sandan Nijeriya ya Magantu kan Umarnin Kotu

Babban Sufeton Ƴan Sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya ce bai saɓa umarnin kotu ba sakamakon ba shi da masaniya kan wani hukunci da kotun ta yanke da ya shafi mayar da wani ɗan sanda kan aikinsa.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar inda tace babban sufeton ya ce an sallami ɗan sandan tun a 1992, shekaru kaɗan bayan shi kansa sufeton ya shiga aikin ɗan sanda.

Ya bayyana cewa hukunci na ƙarshe wanda kotu ta yanke a 2011 zamanin wani sufeto ne daban.

Sai dai Usman Alkali Baba ya ce ya bayar da umarni ga kwamishinan ƴan sanda wanda ke kula da ɓangaren shari’a da ya gudanar da bincike kan wannan zargin domin duba matsayar kotu da kuma ba sufeton shawarar da ta dace ta shari’a domin ɗaukar mataki.

A ɗazu ne Babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta yanke wa Sufeton Ƴan sandan ƙasar hukuncin zaman gidan yari na wata uku.

Mai Shari’a Justice Mobolaji Olajuwon ce ta yanke hukuncin inda ta ce ya saɓa umarnin kotu kamar yadda kafar watsa labarai ta Channels a Najeriya ta ruwaito.

Tun farko dai wani ɗan sanda mai suna Patrick Okoli ne ya shigar da ƙara inda ya ce an yi masa ritaya ƙarfi da yaji a 1992 inda daga baya kotu ta bayar da umarnin a mayar da shi kan aikinsa tare da biyansa duka haƙƙoƙinsa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp