Buhari zai Kaddamar da sabbin Ayyuka a Jihar Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi dake arewa ta tsakiyar Nijeriya ta ayyana ranar Alhamis a matsayin hutu, saboda ziyarar da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai kai Jihar.
Gwamnatin ta ce Buhari zai kai ziyarar ce don bude wasu ayyuka da Gwamnan Jihar, Yahaya Bello ya kammala.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labaran Jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi a Lokoja, babban birnin Jihar.
Gwamnatin jihar ta bukaci al’ummar da su yi fitar farin dango don tarbar Shugaba Buhari.
Kazalika, Gwamnatin ta bukaci kungiyoyin kwadago da masu zaman kansu da jami’an tsaro su tabbatar da zaman lafiya ya wakana a yayin ziyarar ta Buhari.
Buhari dai na ci gaba da ziyartar jihohin Najeriya don kaddamar da ayyuka.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 1 minute 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 43 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com