Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya 10

Saudiyya ta bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗa a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya fitar, ta ce ya zuwa yanzu ƙasar ta samu nasarar kwashe mutum 2, 544.

Sanarwar ta ce cikin mutanen, 119 sun ƙasance ƴan Saudiyya, yayin da 2,425 suka fito daga ƙasashe 74, inda goma daga cikin suka ƙasance ƴan Najeriya.

Ofishin jakadanci ya ce gwamnatin Saudiyya na yin duk mai yiwuwa wajen samarwa ƴan ƙasashen da aka kwashe duk abin da ya kamata, kafin mayar da su ƙasashensu na asali.

Har ila yau, ƙasar ta Saudiyya ta ce za ta yi iya kokarinta wajen ganin ta taimaka wa sauran ƙasashe kwashe mutanensu lami lafiya daga Sudan da kuma ganin an dakatar da faɗan da komawa kan tirba madaidaiciya a ƙasar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 27 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 8 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com