Home DUNIYA Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya...

Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya 10

Saudiyya ta bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗa a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya fitar, ta ce ya zuwa yanzu ƙasar ta samu nasarar kwashe mutum 2, 544.

Sanarwar ta ce cikin mutanen, 119 sun ƙasance ƴan Saudiyya, yayin da 2,425 suka fito daga ƙasashe 74, inda goma daga cikin suka ƙasance ƴan Najeriya.

Ofishin jakadanci ya ce gwamnatin Saudiyya na yin duk mai yiwuwa wajen samarwa ƴan ƙasashen da aka kwashe duk abin da ya kamata, kafin mayar da su ƙasashensu na asali.

Har ila yau, ƙasar ta Saudiyya ta ce za ta yi iya kokarinta wajen ganin ta taimaka wa sauran ƙasashe kwashe mutanensu lami lafiya daga Sudan da kuma ganin an dakatar da faɗan da komawa kan tirba madaidaiciya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp