Home Labarai Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Gwamnatin jihar Kano tace ta shirya tsaf domin gyara yin amfani da baguzen gine-ginen da aka rushe wajen sabunta ginin ganuwar Kano, a kokarin gwamnatin na maido da wuraren tarihi a jihar .

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwar da Sakataren yada labaran gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria,  inda ya ce Abba Kabir Yusuf ya ce za a yi amfani da baraguzen wuraren da aka rushe wajen sake gina Badalar, kuma ana kira ga mutanen da ba su da alaka da inda aka rushe da su guji zuwa wurin domin yan sanda da jami’an hukumar Civil defense ba zasu saurarawa duk wanda aka kama ba.

“Mun zagaya birnin kano domin duba wuraren da aka ruguje, kuma mun yanke shawarar yin amfani da baraguzen wuraren da aka ruguje wajen gyara badalar birnin Kano domin adana tarihi, da kawata Kano da kuma mayar da wuraren wurin yawon bude idanu da dai sauransu”. Engr. Abba Kabir Yusuf yace.

“duk wanda ba ya cikin aikin rusau ya kamata ya nisanta kansa daga wurin, domin hukumomin tsaro ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakan da suka dace kan masu kutse da kuma wadanda suke sabawa ka’ida.” A cewar Abba Gida-gida

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda tare da kai rahoto ga jami’an tsaro domin ci gaban zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp