Home DUNIYA ‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

Wata sabuwar kididdiga ta duniya ta bayyana cewa, kimanin ‘yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci, yayin da aka bayyana jihar Yobe a matsayin wadda ta fi fama da yunwa a kasar.

Tonye Cole, dan takarar gwamnan jihar Rivers karkashin jam’iyyar APC da ya gabatar da makala a wani taron ranar tunawa da yaki da yunwa ta duniya a birnin Abuja, ya bayyana cewa, wasu alkaluman Majalisar Dinkin Duniya sun ce, mutane dubu 25 ne ke mutuwa a kowacce rana sakamakon yunwa da suka hada da kananan yara dubu 10 a duniya.

Cole ya kuma bayyana cewa, Hukumar Kididdiga ta Najeriya ta kiyasta mutane miliyan 133 da ke fama da nau’uka daban-daban na yunwa a kasar.

Ya ce, ya zama dole Najeriya ta dauki mataki domin tunkarar wannan matsalar ta bakin talauci a Najeriya.

Kwararru sun ce akwai wasu dalilai da ke haddasa talauci a Najeriya kamar rikice-rikice da gurbatacciyar gwamnati da rashin ingancin tsarin kiwon lafiya da suka ce ya zama dole a magance su cikin gaggawa muddin ana son kawar da yunwa a kasar.

Jihar Yobe ce ta fi fama da matsalar yunwa a Najeriya, inda take da kashi 44.2, sannan jihar ce ke kan gaba taa fuskar samun matsalar rashin abinci mai gina jiki, inda a wannan bangaren take da maki 27.4 kamar yadda masana suka bayyana.

Sai kuma jihohin Zamfara da Kebbi da Jigawa da ke biye da Yobe wajen samun wannan matsalar ta fatara da yunwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp