Home DUNIYA ‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

Wata sabuwar kididdiga ta duniya ta bayyana cewa, kimanin ‘yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci, yayin da aka bayyana jihar Yobe a matsayin wadda ta fi fama da yunwa a kasar.

Tonye Cole, dan takarar gwamnan jihar Rivers karkashin jam’iyyar APC da ya gabatar da makala a wani taron ranar tunawa da yaki da yunwa ta duniya a birnin Abuja, ya bayyana cewa, wasu alkaluman Majalisar Dinkin Duniya sun ce, mutane dubu 25 ne ke mutuwa a kowacce rana sakamakon yunwa da suka hada da kananan yara dubu 10 a duniya.

Cole ya kuma bayyana cewa, Hukumar Kididdiga ta Najeriya ta kiyasta mutane miliyan 133 da ke fama da nau’uka daban-daban na yunwa a kasar.

Ya ce, ya zama dole Najeriya ta dauki mataki domin tunkarar wannan matsalar ta bakin talauci a Najeriya.

Kwararru sun ce akwai wasu dalilai da ke haddasa talauci a Najeriya kamar rikice-rikice da gurbatacciyar gwamnati da rashin ingancin tsarin kiwon lafiya da suka ce ya zama dole a magance su cikin gaggawa muddin ana son kawar da yunwa a kasar.

Jihar Yobe ce ta fi fama da matsalar yunwa a Najeriya, inda take da kashi 44.2, sannan jihar ce ke kan gaba taa fuskar samun matsalar rashin abinci mai gina jiki, inda a wannan bangaren take da maki 27.4 kamar yadda masana suka bayyana.

Sai kuma jihohin Zamfara da Kebbi da Jigawa da ke biye da Yobe wajen samun wannan matsalar ta fatara da yunwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp