Home Labarai Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Gwamnatin jihar Kano tace ta shirya tsaf domin gyara yin amfani da baguzen gine-ginen da aka rushe wajen sabunta ginin ganuwar Kano, a kokarin gwamnatin na maido da wuraren tarihi a jihar .

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwar da Sakataren yada labaran gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria,  inda ya ce Abba Kabir Yusuf ya ce za a yi amfani da baraguzen wuraren da aka rushe wajen sake gina Badalar, kuma ana kira ga mutanen da ba su da alaka da inda aka rushe da su guji zuwa wurin domin yan sanda da jami’an hukumar Civil defense ba zasu saurarawa duk wanda aka kama ba.

“Mun zagaya birnin kano domin duba wuraren da aka ruguje, kuma mun yanke shawarar yin amfani da baraguzen wuraren da aka ruguje wajen gyara badalar birnin Kano domin adana tarihi, da kawata Kano da kuma mayar da wuraren wurin yawon bude idanu da dai sauransu”. Engr. Abba Kabir Yusuf yace.

“duk wanda ba ya cikin aikin rusau ya kamata ya nisanta kansa daga wurin, domin hukumomin tsaro ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakan da suka dace kan masu kutse da kuma wadanda suke sabawa ka’ida.” A cewar Abba Gida-gida

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda tare da kai rahoto ga jami’an tsaro domin ci gaban zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp