Home Labarai Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Za mu sabunta ginin ganuwar Kano – Abba Gida-gida

Gwamnatin jihar Kano tace ta shirya tsaf domin gyara yin amfani da baguzen gine-ginen da aka rushe wajen sabunta ginin ganuwar Kano, a kokarin gwamnatin na maido da wuraren tarihi a jihar .

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwar da Sakataren yada labaran gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria,  inda ya ce Abba Kabir Yusuf ya ce za a yi amfani da baraguzen wuraren da aka rushe wajen sake gina Badalar, kuma ana kira ga mutanen da ba su da alaka da inda aka rushe da su guji zuwa wurin domin yan sanda da jami’an hukumar Civil defense ba zasu saurarawa duk wanda aka kama ba.

“Mun zagaya birnin kano domin duba wuraren da aka ruguje, kuma mun yanke shawarar yin amfani da baraguzen wuraren da aka ruguje wajen gyara badalar birnin Kano domin adana tarihi, da kawata Kano da kuma mayar da wuraren wurin yawon bude idanu da dai sauransu”. Engr. Abba Kabir Yusuf yace.

“duk wanda ba ya cikin aikin rusau ya kamata ya nisanta kansa daga wurin, domin hukumomin tsaro ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakan da suka dace kan masu kutse da kuma wadanda suke sabawa ka’ida.” A cewar Abba Gida-gida

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bin doka da oda tare da kai rahoto ga jami’an tsaro domin ci gaban zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp