Home DUNIYA RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

Gidan rediyon RFI da gidan talabijin na France 24 sun yi Allah-wadai da matakin da hukumomin sojin Nijar suka dauka na dakatar da su daga yada shirye-shiryensu a kasar, mako guda da juyin mulkin da sojojin suka yi a kasar.

Hukumar Gudanarwa kafofin yada Faransa a kasashen ketare ta France Medias Monde ta bayyana matakin a matsayin wanda ya yi hannun riga da dokokin shari’a, lamarin da ta ce zai dakile wa ‘yan kasar hanyoyin da suke samun cikakkun labarai cikin ‘yanci.

Wannan na zuwa ne bayan irin wannan dakatarwar da sojojin da ke mulki a Mali da Burkina Faso suka yi wa RFI da France 24 a watannin da suka shude.

Hukumar ta France Medias Monde ta jaddada kudirinta ga ‘yancin yada labarai da kuma kare lafiyar ‘yan jaridarta.

RFI na yada shirye-shiryensa a tashoshin FM guda bakwai baya ga gajeren zango da sauran hanyoyin tauraron dan adam cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde.

Kazalika akwai wasu karin gidajen rediyo 44, abokan huldar RFI da su ma ke yada shirye-shiryensa cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde a Nijar.

A shekarar 2022, wasu alkaluma da aka tattara sun nuna cewa, kimanin masu saurare miliyan 1 da dubu 900 ne ke sauraren RFI a kowanne mako a kasar ta Nijar, wato kwatankwacin kashi 18 na daukacin al’ummar kasar, yayin da RFI din ke zama kafar yada labarai ta ketare mafi girma a kasar kamar yadda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a ta nuna.

Har ila yau, alkaluman sun nuna cewa, kimanin rubu’in daukacin jama’ar Nijar ne suka bibiyar tashar ta RFI a kowanne mako a shekarar bara.

Koda yake har yanzu ana iya samun RFI da France 24 ta hanyoyin tauraron dan adam kai tsaye kamar su Eutelsat da Arab-Sat, sai kuma gajeren zango.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp