Home DUNIYA Gwamnatin Nijeriya ta Magantu kan batun Auren jinsi a kasar

Gwamnatin Nijeriya ta Magantu kan batun Auren jinsi a kasar

Gwamnatin Najeriya ta sake jaddada cewar babu batun luwaɗi da maɗigo a cikin yarjejeniyar Samoa da suka sanya hannu akai a ƙarshen watan yunin da ya gabata, kamar yadda wasu ƴan ƙasar ke zargi.

Ministan watsa labaran  Muhammmad Idris ya shaidawa hakan, inda yace yarjejeniyar ta kunshi ayyukan ci gaban al’umma ne, kuma an yi ta ne a tsakanin ƙasashen Afrika da na yankin Caribbean, da mutanen Pacific wato OACPS.

Haka kuma Minisitan yada labaran Muhammmad Idris ya ce akwai wata yarjenejiya mai suna OACPS da ta samu goyon bayan ƙasashen Turai da suka sa mata hannu a lokacin da ake taron majalisar ɗinkin duniya na 73.

Ya ci gaba da cewa “Akwai ƙa’idoji har 103 da aka cimma kan wannan yarjejeniya, amma babban al’amari da ya kamata a fahimta a nan shi ne, an yi waɗannan yarjejeniyar ne bisa tsarin shari’a da zai ba da damar haɗin gwiwa tsakanin OACPS da Tarayyar Turai domin cigaban al’umma, da dakile sauyin yanayi, da samar da kuɗaɗen zuba jari, ba wai yadda mutane ke ta yaɗawa ba.

Muhammad Idris ya ce ‘Ko kadan babu gaskiya a cikin wannan zargi, don kafin su saka hannun kan waɗannan ƙa’idoji 103 sai da aka kafa kwamiti da ya yi taza da tsifa a kansu, wanda ministan kasafin kuɗi Atiku Bagudu ne ya jagoranci kwamitin, sannan akwai ministan harkokin wajen Najeriya, da Ministan shari’a wanda kuma sai da suka tabbatar da cewar babu wata ƙa’ida daga cikin ƙa’idojin da ta ci karo da dokokin Najeriya sannan aka amice da saka hannun” in ji ministan.

Haka kuma ya ce “ya zama wajibi mu tabbatar wa da ‘yan Najeriya cewar Najeriya, da gwamnatin Bola Tinubu ba za ta saka hannu kan wata yarjejeniya ba da za ta ci karo da muradan mutanenten ƙasar nan ba ” A cewar Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris.

A ranar Laraba ne wasu rahotonni suka ambato cewa gwamnatin tarayya ta saka hannu kan yarjejeniyar, wadda ta ƙunshi wasu alƙawurra tsakanin ƙasashen Tarayyar Turai, da gamayyar ƙasashen yankin Karebiya da na Pacific.

Rahotonnin sun ambato cewa baya ga ayyukan raya ƙasa da cigaban al’umma, yarjejeniyar ta kuma ƙunshi batun amincewa da gwagwarmayar neman ‘yanci da masu fafutikar luwaɗi da maɗigo ke yi a ƙasashen.

A shekarar 2014 Najeriya ta amince da dokar haramta alaƙar aure tsakanin jinsi ɗaya, abin da ke nufin luwaɗi da maɗigo haramtattu ne a ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp