Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar –...

Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar – Lagbaja

Shugaban sojojin Nijeriya Laftanal Janar Taoreed Lagbaja yace dakarun dake yaki da ayyukan ta’addanci da sauran lamaurran da suka shafi tsaro a yankin Arewa maso gabashin kasar na samun gagarumar nasara.

Lagbaja ya bayyana hakan ne a ranar alhamis a garin Jos, yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangare na bikin cikar shekara da rundunar ta shirya.

ya dora alhakin harin kunar baki wake a Gwozo bisa hare haren da dakarun sojoji suka din gi kaiwa kan mabambanta gungun ‘yan ta’addan a yakin na arewa maso gaba.

yace: “Ana sake samun nasarori bisa yadda dakarun ke cigaba da matsa kaimi da kuma wasu hare hare kan ‘yan ta’addan dake yankin.

Ya kara da cewa sun sami bayanan sirri dake nuna yadda ‘yan Ta’addan suka shirya kai hare-hare kunar bakin wake har guda 15 amma 3 ne kawai suka sami nasara.

“Dakrun mu sun yi dukkanin mai yiwuwa don gani sun kawar da makiya.

“Don haka, ina kira ga Al’ummar Nijeriya da su zama masu taimakawa harkokin tsaro, zamu tabbatar da bincikar dukkanin wani taron al’umma,” a cewar sa.

ya bayyana yaki da rashin tsaro matsayin abinda ke bukatar hada karfi da karfe, “don haka ya kamata mu dauke shi da matukar muhimmanci”.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp