Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar –...

Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar – Lagbaja

Shugaban sojojin Nijeriya Laftanal Janar Taoreed Lagbaja yace dakarun dake yaki da ayyukan ta’addanci da sauran lamaurran da suka shafi tsaro a yankin Arewa maso gabashin kasar na samun gagarumar nasara.

Lagbaja ya bayyana hakan ne a ranar alhamis a garin Jos, yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangare na bikin cikar shekara da rundunar ta shirya.

ya dora alhakin harin kunar baki wake a Gwozo bisa hare haren da dakarun sojoji suka din gi kaiwa kan mabambanta gungun ‘yan ta’addan a yakin na arewa maso gaba.

yace: “Ana sake samun nasarori bisa yadda dakarun ke cigaba da matsa kaimi da kuma wasu hare hare kan ‘yan ta’addan dake yankin.

Ya kara da cewa sun sami bayanan sirri dake nuna yadda ‘yan Ta’addan suka shirya kai hare-hare kunar bakin wake har guda 15 amma 3 ne kawai suka sami nasara.

“Dakrun mu sun yi dukkanin mai yiwuwa don gani sun kawar da makiya.

“Don haka, ina kira ga Al’ummar Nijeriya da su zama masu taimakawa harkokin tsaro, zamu tabbatar da bincikar dukkanin wani taron al’umma,” a cewar sa.

ya bayyana yaki da rashin tsaro matsayin abinda ke bukatar hada karfi da karfe, “don haka ya kamata mu dauke shi da matukar muhimmanci”.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp