Home DUNIYA Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar –...

Sojojin Nijeriya sun sami gagarumar nasara a Arewa maso gabashin kasar – Lagbaja

Shugaban sojojin Nijeriya Laftanal Janar Taoreed Lagbaja yace dakarun dake yaki da ayyukan ta’addanci da sauran lamaurran da suka shafi tsaro a yankin Arewa maso gabashin kasar na samun gagarumar nasara.

Lagbaja ya bayyana hakan ne a ranar alhamis a garin Jos, yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangare na bikin cikar shekara da rundunar ta shirya.

ya dora alhakin harin kunar baki wake a Gwozo bisa hare haren da dakarun sojoji suka din gi kaiwa kan mabambanta gungun ‘yan ta’addan a yakin na arewa maso gaba.

yace: “Ana sake samun nasarori bisa yadda dakarun ke cigaba da matsa kaimi da kuma wasu hare hare kan ‘yan ta’addan dake yankin.

Ya kara da cewa sun sami bayanan sirri dake nuna yadda ‘yan Ta’addan suka shirya kai hare-hare kunar bakin wake har guda 15 amma 3 ne kawai suka sami nasara.

“Dakrun mu sun yi dukkanin mai yiwuwa don gani sun kawar da makiya.

“Don haka, ina kira ga Al’ummar Nijeriya da su zama masu taimakawa harkokin tsaro, zamu tabbatar da bincikar dukkanin wani taron al’umma,” a cewar sa.

ya bayyana yaki da rashin tsaro matsayin abinda ke bukatar hada karfi da karfe, “don haka ya kamata mu dauke shi da matukar muhimmanci”.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp