Home DUNIYA Jihohi Nijeriya 18 ka iya fuskanta ambaliyar

Jihohi Nijeriya 18 ka iya fuskanta ambaliyar

Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi jihohin ƙasar 18 kan barazanar ɓarkewar cutar Kwalara saboda barazanar fuskantar ambaliya, sakamakon ci gaba da ruwan sama da ake yi a jihohin.

Ministan ruwa da tsaftar muhalli na ƙasar, Joseph Terlumum ne ya bayyana damuwar a lokacin da yake jawabi ga taron manema labarai ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce kawo yanzu mutum 63 ne suka mutu sakamakon bullar cutar, yayin da aka samu mutum 1,102 da ake zargi sun kamu da cutar.

Mamakon ruwan sama da ake samu a baya-bayan nan a wasu jihohin ƙasar na ƙara fargaba a zukatan jama’a kan ƙara bazuwar cutar, lamarin da ya sa ministan ya yi kira ga jihohin da su ƙara ƙaimi wajen tsaftace magudanar ruwa, don kauce wa ambaliya.

“Muna kira ga jihohi da ƙananan hukumomi su ƙara ƙaimi wajen tsaftace muhalli domin kauce wa ambaliya da sauran bala’o’in da ke tattare da ambaliya, kamar cutar kwalara”.

Jihohin da ministan ya ce suna fuskantar barazanar ambaliyar sun haɗa da; Akwa Ibom da Anambra da Adamawa da Benue da Bayelsa da Cross River da Delta da Edo da Jigawa da Kogi da Kebbi da Kaduna da Niger da Nasarawa da Ondo da Ogun da Rivers da Taraba da luma birnin tarayya Abuja.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp