Home DUNIYA Jihohi Nijeriya 18 ka iya fuskanta ambaliyar

Jihohi Nijeriya 18 ka iya fuskanta ambaliyar

Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi jihohin ƙasar 18 kan barazanar ɓarkewar cutar Kwalara saboda barazanar fuskantar ambaliya, sakamakon ci gaba da ruwan sama da ake yi a jihohin.

Ministan ruwa da tsaftar muhalli na ƙasar, Joseph Terlumum ne ya bayyana damuwar a lokacin da yake jawabi ga taron manema labarai ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce kawo yanzu mutum 63 ne suka mutu sakamakon bullar cutar, yayin da aka samu mutum 1,102 da ake zargi sun kamu da cutar.

Mamakon ruwan sama da ake samu a baya-bayan nan a wasu jihohin ƙasar na ƙara fargaba a zukatan jama’a kan ƙara bazuwar cutar, lamarin da ya sa ministan ya yi kira ga jihohin da su ƙara ƙaimi wajen tsaftace magudanar ruwa, don kauce wa ambaliya.

“Muna kira ga jihohi da ƙananan hukumomi su ƙara ƙaimi wajen tsaftace muhalli domin kauce wa ambaliya da sauran bala’o’in da ke tattare da ambaliya, kamar cutar kwalara”.

Jihohin da ministan ya ce suna fuskantar barazanar ambaliyar sun haɗa da; Akwa Ibom da Anambra da Adamawa da Benue da Bayelsa da Cross River da Delta da Edo da Jigawa da Kogi da Kebbi da Kaduna da Niger da Nasarawa da Ondo da Ogun da Rivers da Taraba da luma birnin tarayya Abuja.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp