Home DUNIYA Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad Tinubu ya kafa sabuwar Ma’aikatar Harkokin Kiwon Dabbobi a Nijeriya.

wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake tsaka da rikici a zauren majalisar kasar kan yadda makiyaya zasu gudanar da harkokin kiwo a kasar.

Bola Tinubu ya sanar da hakan ne lokacin da ya ke kaddamar da kwamitin da zai gyara tsarin kiwo, Kwamitin da zai yi aiki wajen magance matsaloli tsakanin manoma da makiyaya,

A taron da ya sami halartar, mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, da kuma wasu jami’an gwamnati.

A watan Satumban 2023, Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin shugaban ƙasa don gyaran bangaren kiwo da magance rikice-rikicen makiyaya da manoma.

Wannan shawarar ta biyo bayan rahoton taron kasa kan gyara tsarin kiwo da rage rikice-rikicen da ke da nasaba da kiwo a Najeriya.
Kungiyar Miyetti Allah ta MACBAN, ta buƙace shugaban ƙasa ya ƙirƙiro ma’aikatar kiwo.

Shugabansu, Alhaji Baba Usman Ngelzarma, ya ce makiyaya na buƙatar ma’aikata mai zaman kanta da za ta kula da dukkanin al’amuran da suka shafi kiwo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp