Tinubu ya ba kowanne Gwamna shinkafa tirela 20 a raba wa talakawa

Gwamnatin Tarayya ta ayyana raba shinkafa tirela 20 ga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja, domin rabawa ga mabukata.

Za a raba kayan abincin ne a faɗin kasar a masatyin wani matsaki na kawar da matsalar yunwa da ke addabar kasar.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan ga manema labaran fadar Shugaban Kasa a ranar Litinin, jim kadan bayan fitowa daga taron Majalisar Zartawa wanda Shugaban Kasar, Bola Tinubu ya jagoranta.

Ministan ya ce majalisar ta fahimci yadda matsalar karancin abincin ke addabar ’yan kasar, don hakan ta amince da raba shinkafa tirela 20 ga kowacce jiha da Abuja ga mabukata.

Al’ummar Nijeriya dai na fama da matsalar tsadar abinci, abin da suka alakanta da cire tallafin man fetur da gwamnatin Tinubu ta yi.

Matakin dai ya haifar da tashin farashin kayan masarufi da kayan amfanin yau da kullum a kasar da ke da arzikin man fetur da ma’adinan a karkashin kasa.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 29 minutes 29 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 10 minutes 54 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com