Home DUNIYA Gwamnatin Tinubu zata fara bawa dalibai bashin da suka nema

Gwamnatin Tinubu zata fara bawa dalibai bashin da suka nema

Gwamnatin tarayya za ta fara bayar da bashin karatu ga manyan makarantun gwamnatin tarayya kasar da suka nemi bashin nan da mako mai zuwa.

Sai dai shugaban asusun, Akintunde Sawyerr, ya ce ɗaliban makarantun da za su fara sabon zangon karatu ne kawai za su ga kuɗin a asusunsu a yanzu.

A jiya Laraba ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da asusun mai suna Nigerian Education Loan Fund (Nelfund) a hukumance a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Mista Sawyerr ya ce jimillar ɗalibai 170,000 ne suka yi rajista da asusun, waɗanda suka ƙunshi ɗaliban jami’a, da na kwalejojin ilimi da fasaha.

“A taƙaice dai, jimillar ɗalibai 110,000 ne suka nemi bashin. Sun ba da bayanansu tare da miƙa takardun neman, kuma su ne suka cancanta. Amma duk da haka za mu ƙara gudanar da bincike a kansu… Amma da alama sama da mutum 110,000 ne za su fara samun bashin a sati mai zuwa,” in ji shi.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp