Na roke ku kada ku shiga zanga – zanga – Kwamishinan ‘Yan sandan Abuja

Rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja ta bukaci matasan birni dasu karacewa shiga zanga-zanga da wasu ke shirin shiryawa a birni.

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin, Benneth Igweh, ne ya bukaci hakan, inda yace su kauracewa shiga zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a farkon watan Agusta kan matsalar tsadar rayuwa da ta addabi Yan Nigeria.

Igwe ya bayyana haka ne Lokacin da ya ke ganawa da manema labaru a Birnin Abuja yayin da aka gurfanar da wadansu da ake zargi da aikata laifuka daban daban a yankin.

Kwamishinan ya ce ya na tsoron Kar masu aikata laifuka su yi amfani da damar zanga-zangar don kawo barazana ga tsaro da kuma lalata duniyar alumma.

Ya ci gaba da cewa jami’an tsaro na birnin tarayya na aiki ba dare ba rana don tabbatar da tsaro a yankin, in da ya ce suna bin batagari har wasu jihohi makota musamman wadanda ke zamantowa barazanane ga yankin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 17 hours 37 minutes 45 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 19 hours 19 minutes 10 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com