Home General Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.
Shugaban Ƙungiyar shuwagabannin Matasan Najeriya Kwamared Murtala Mohammed Gamji ne ya sanar da hakan, ta cikin wani taron manema labarai da suka gudanar yau a Abuja, inda ya ce sun janye ƙudirin nasu ne a sakamakon yadda suka yi zargin sheɗanci ya shigo cikin shirin nasu.
Jaridar GTR ta ruwaito Gamji na cewa sun ɗauki matakin ne biyo bayan yadda suka gano wasu ɓata gari suna shirya wani mummunan abu, ta hanyar fakewa da zanga-zangar domin rikita ƙasar gaba-ɗaya.
A cewar Gamji ” Ni na fara shirya zanga-zangar kuma wasu mutane sun gayyace ni mun zauna dasu, harma suka shaida min so suke ayi zanga-zangar a iya Jihar Kaduna da Jos da kuma Babban birnin tarayya Abuja, saboda haka dole mu janye shirin namu tunda wasu sun fara yunƙurin cimma burinsu ta hanyar yin amfani damu”.
domin haka ya ce suna kira da dukkan wani ɓangare na al’ummar dake yankin arewa da suyi watsi dayin zanga-zangar, su dawo a haɗa kai abi hanyoyin da suka dace domin neman haƙƙin talakawan ƙasar a wurin shugabanni.
Bugu da ƙari ya kuma shawarci Jami’an tsaro da suyi gaggawar kama dukkan waɗanda suka fito zanga-zangar, domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a dukkan sassan Najeriya.
A ƙarshe ya jaddada cewa suna barranta kansu da yadda ake zagin Malamai, dama yunƙurin fakewa da zanga-zangar wajen lalata dukiyar mutane koma ƙona kayan Gwamnati wanda babu abinda zai haifar illa ƙarin wasu matsaloli a faɗin ƙasar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp