Home General Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.
Shugaban Ƙungiyar shuwagabannin Matasan Najeriya Kwamared Murtala Mohammed Gamji ne ya sanar da hakan, ta cikin wani taron manema labarai da suka gudanar yau a Abuja, inda ya ce sun janye ƙudirin nasu ne a sakamakon yadda suka yi zargin sheɗanci ya shigo cikin shirin nasu.
Jaridar GTR ta ruwaito Gamji na cewa sun ɗauki matakin ne biyo bayan yadda suka gano wasu ɓata gari suna shirya wani mummunan abu, ta hanyar fakewa da zanga-zangar domin rikita ƙasar gaba-ɗaya.
A cewar Gamji ” Ni na fara shirya zanga-zangar kuma wasu mutane sun gayyace ni mun zauna dasu, harma suka shaida min so suke ayi zanga-zangar a iya Jihar Kaduna da Jos da kuma Babban birnin tarayya Abuja, saboda haka dole mu janye shirin namu tunda wasu sun fara yunƙurin cimma burinsu ta hanyar yin amfani damu”.
domin haka ya ce suna kira da dukkan wani ɓangare na al’ummar dake yankin arewa da suyi watsi dayin zanga-zangar, su dawo a haɗa kai abi hanyoyin da suka dace domin neman haƙƙin talakawan ƙasar a wurin shugabanni.
Bugu da ƙari ya kuma shawarci Jami’an tsaro da suyi gaggawar kama dukkan waɗanda suka fito zanga-zangar, domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a dukkan sassan Najeriya.
A ƙarshe ya jaddada cewa suna barranta kansu da yadda ake zagin Malamai, dama yunƙurin fakewa da zanga-zangar wajen lalata dukiyar mutane koma ƙona kayan Gwamnati wanda babu abinda zai haifar illa ƙarin wasu matsaloli a faɗin ƙasar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp