Home General Gwamnatin jihar Katsina na shirin samar da Dokar “Iddah” ga matan Jihar

Gwamnatin jihar Katsina na shirin samar da Dokar “Iddah” ga matan Jihar

Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya na kokarin samar da wata sabuwar dokar kan iddar mata Mai suna “Iddah Period Law”, domin baiwa mata ma’aikatan gwamnati damar zama a gida na tsawon wata hudu da kwana goma idan mazajensu suka rasu.

Shugaban ma’aikatan jihar Katsina, Alhaji Falalu Bawale ne ya bayyana haka yayin da yake ganawa da manema labarai.

A cewarsa, gabatar da sabuwar dokar ya biyo bayan kudurin da majalisar dokokin jihar ta gabatar, inda ta bukaci gwamnatin jihar ta duba batun wa’adin Iddah wanda hukumar zartaswa ta amince da shi , tare da yin aiki da shawarwarin da majalisar zartaswa ta gabatar.

Ya kara da cewa, tuni aka fitar da wata takarda ga dukkan ma’aikatun Jihar da na Kananan hukumomin domin baiwa mata ma,aikata damar gudanar da iddah a lokacin da bukatar hakan ta taso.

wannan dai na zuwa ne dai dai da Lokacin da Dan Majalisar tarayya na jamiyyar APC daga jihar Niger ya gabatar da wani kudiri makamancin haka na neman ba wa matan da mazansu suka rasu damar tafiya hutu tare da cikakken albashin ma’auratan da suka rasu, inda kudurin ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

Iddah ga matan da mazajen su suka mutu na guda cikin sharuddan da addinin muslunci yayiwa mata a yayin gudanar da ruyuwarsu ta yau da kulum muddin dai bukatar hakan ta taso.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp