Home Labarai ƙyandar biri ta kama Mutum 39 a Najeriya

ƙyandar biri ta kama Mutum 39 a Najeriya

Gwamnatin Najeriya ta ce ta tsaurara matakan bincike a dukkan hanyoyin shigarta domin daƙile yiwuwar shiga da cutar ƙyandar biri cikin ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan hukumar hana yaɗuwar cutuka ta Afirka, da ma Majalisar Dinkin Duniya sun ƙaddamar da dokar ta ɓaci a kan yaƙi da cutar ta ƙyandar biri da ake kira da Mpox.

Da yake sanar da matakan da hukumomi a Najeriyar ke ɗauka domin kare jama’a daga wannan cuta, ministan lafiya Farfesa Muhammad Pate, ya ce za a tsaurara bincike a kan masu shiga Najeriya daga kowanne ɓangare, domin tabbatar da ganin wani daga waje bai shigar da ƙwayar cutar cikin ƙasar ba.

Sanarwar da Ministan ya fitar ta ce cibiyar daƙile yaɗuwar cutuka ta ƙasar ta sanar da gwamnati da cewa an samu mutum 39 da suka kamu da cutar ƙyandar biri a Najeriya.

Ministan ya ce daga alƙalumman da hukumomi suka tattara daga farkon wannan shekarar, an samu masu cutar ne a jihohi 33 da birnin tarayya Abuja, kuma kawo yanzu babu wanda ya mutu sanadiyyar cutar.

Saboda haka ne ministan ya ce gwamnati ta yi saurin samar da tsarin yin gwaji ga duk wanda zai shiga Najeriya, domin gano cutar tun kafin a shigar masu da annoba.

Itama hukumar hana yaduwar cutuka ta Najeriyar ta jaddada wannan matakin da gwamnatin tarayyar ta sanar, kuma shugaban ta Dr Jide Idris, ya yi bayanin cewa sun ƙara matakan yin gwaji a filayen jiragen saman ƙasa da ƙasa guda 5 da ake da su a ƙasar, da tashoshin ruwa 10 da kuma iyakokin kan ƙasa guda 51, duk dai a ƙoƙarin hana shiga da cutar.

Hukumomi a Najeriyar dai sun kuma sanar da tsaurara matakan tantance masu ɗauke da cutar a jihohin Lagos da Enugu da Rivers da Cross Rver da Akwa Ibom da kuma Adamawa.

Sauran jihohin sun haɗa da Taraba da Kano da kuma birnin tarayya Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp