Home Labarai ‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

Rahotannin daga jihar Benuwai a Arewa maso tsakiyar Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da wani ɗalibin likitanci mai sanin makamar aiki a jihar da ke fama da matsalar ƴan bindiga.

An kai wa ɗaliban harin ne a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Kudu maso Gabashin Jihar Enugu a ranar 15 ga watan domin halartar taron Ƙungiyar Ɗaliban Likitanci na shekara-shekara.

“Daliban, waɗanda aka ce ƴan Jami’ar Maiduguri da Jami’ar Jos ne, suna tafiya ne a tare, inda ƴan bindigar suka afka musu da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a yankin Otukpo na jihar.”

Kakakin Rundunar ‘Yan sanda, Catherine Anene, ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Harkar garkuwa da mutane ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda lamarin ya fara zama ruwan dare a ƙasar ta Afirka ta Yamma.

A watan Mayu, ƴan bindiga sun kashe mutum 11, sannan suka sace wasu da ba a tantance adadinsu ba a Ƙaramar Hukumar Agatu ta Jihar Benue.

Haka kuma a Janairu, aƙalla fasinjoji guda 45 ne aka sace a lokacin da ƴan bindiga suka tare wasu motoci a kan hanyar Otukpo-Enugu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp