Home General Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir-Yusuf ya gabatar da karin kasafin kudi naira biliyan 99.2 na shekarar 2024 ga majalisar dokokin kasar domin amincewa.

An gabatar da bukatar ne a cikin wata wasika da aka karanta a yayin zaman majalisar wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta.

Gwamnan ya nemi amincewar majalisar ne a karkashin sashe na 122 (A da B) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 don gudanar da ayyuka da nufin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi Musa Shanono ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2024 na farko ya kai Naira biliyan 437.3, idan aka kara da wannan karin kasafin ya kai jimillar Naira biliyan 536.5.

Shanono ya jaddada cewa karin kasafin kudin zai kunshi sabon tsarin biyan mafi karancin albashi, samar da ababen more rayuwa, bunkasa rayuwar jama’a da dai sauran muhimman abubuwa.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnati na mai da hankali kan wadannan fannoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp