Home General Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir-Yusuf ya gabatar da karin kasafin kudi naira biliyan 99.2 na shekarar 2024 ga majalisar dokokin kasar domin amincewa.

An gabatar da bukatar ne a cikin wata wasika da aka karanta a yayin zaman majalisar wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta.

Gwamnan ya nemi amincewar majalisar ne a karkashin sashe na 122 (A da B) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 don gudanar da ayyuka da nufin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi Musa Shanono ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2024 na farko ya kai Naira biliyan 437.3, idan aka kara da wannan karin kasafin ya kai jimillar Naira biliyan 536.5.

Shanono ya jaddada cewa karin kasafin kudin zai kunshi sabon tsarin biyan mafi karancin albashi, samar da ababen more rayuwa, bunkasa rayuwar jama’a da dai sauran muhimman abubuwa.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnati na mai da hankali kan wadannan fannoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp