Home General Ambaliya – Gwamnatin Adamawa ta umarci wasu garuruwa su tashi

Ambaliya – Gwamnatin Adamawa ta umarci wasu garuruwa su tashi

Gwamnatin jihar Adamawa ta gargardi mutanen garuruwan dake fuskantar yuwuwar aukuwar ambaliyar ruwa gargadi da su gaggauta tashi su koma tudu domin kaucewa asarar rayuka da dukiya.

Babbar daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (ADSEMA) Dr. Celine Laori ce ta yi gargadin a yayin da take ganawa da kamfanin dillanci labarai na NAN a garin Yola dake jihar.

Tace mammakon ruwan saman da ake makawa a kananan hukumomi uku da suka hadar da Madagali, Demsa, da kuma Numan sun isa izina ga mutanen da ke rayuwa a kwari ka iya fuskantar barazanar amfaliyar.

Laori ta kara da cewa ambaliyar ruwan ta shafi garuruwa 21 dake karkashin kananan hukumomi uku, wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane shida tare da raba sama da 12,961.

“Ambaliyar ta shafi harkokin yau da kullum na mutane, ta lalata Gadoji, Gidaje, Shaguna, Wuraren kula da lafiya, Makarantu, Gonaki da sauransu.”

“A Madagali kadai, ambaliyar ta shafi mutane sama da 10,264 a garuruwa 11 wanda mutane ke cigaba da karbar kulawa a sansanoni tara mabambanta.

“A Numan, ta Shafi mutane 1,113 inda ta raba 206 da muhallin su a garuruwa biyar, wanda yanzu haka suke zaune a sansanoni 2, haka ma a Demsa ta shafi mutane 1,582 a garuruwa biyar.

Laori ta kara da cewa gwamnatin jihar ta dauki matakin gaggawa na samarwa wadanda iftila’in ya rutsa da su tallafin da ya hadar da na Abinci, da wadanda ba na ci ba, da suka hadar da Shinkafa, Maize, Man Gyada, Abin shinfida, bokita, Magani, kayan sawa na manay da na yara.

Daga bisani tayi kira ga sarakunana gargajiya da su yawa da kokarin gwamnati ta hanyar wayar da kan Al’umma don tseratar da rayukan su, ta kuma bukaci kungiyoyi masu zaman kansu da masu hannu da shuni da su tallafawa yunkurin Gwamnatin wajen samawa al’ummar da suka fada cikin iftila’in Abinci.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp