Home General Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir-Yusuf ya gabatar da karin kasafin kudi naira biliyan 99.2 na shekarar 2024 ga majalisar dokokin kasar domin amincewa.

An gabatar da bukatar ne a cikin wata wasika da aka karanta a yayin zaman majalisar wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta.

Gwamnan ya nemi amincewar majalisar ne a karkashin sashe na 122 (A da B) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 don gudanar da ayyuka da nufin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi Musa Shanono ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2024 na farko ya kai Naira biliyan 437.3, idan aka kara da wannan karin kasafin ya kai jimillar Naira biliyan 536.5.

Shanono ya jaddada cewa karin kasafin kudin zai kunshi sabon tsarin biyan mafi karancin albashi, samar da ababen more rayuwa, bunkasa rayuwar jama’a da dai sauran muhimman abubuwa.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnati na mai da hankali kan wadannan fannoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp