Home General Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan Kano ya aikawa Majalisar jihar Karin Kasafi

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir-Yusuf ya gabatar da karin kasafin kudi naira biliyan 99.2 na shekarar 2024 ga majalisar dokokin kasar domin amincewa.

An gabatar da bukatar ne a cikin wata wasika da aka karanta a yayin zaman majalisar wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta.

Gwamnan ya nemi amincewar majalisar ne a karkashin sashe na 122 (A da B) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 don gudanar da ayyuka da nufin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi Musa Shanono ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2024 na farko ya kai Naira biliyan 437.3, idan aka kara da wannan karin kasafin ya kai jimillar Naira biliyan 536.5.

Shanono ya jaddada cewa karin kasafin kudin zai kunshi sabon tsarin biyan mafi karancin albashi, samar da ababen more rayuwa, bunkasa rayuwar jama’a da dai sauran muhimman abubuwa.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnati na mai da hankali kan wadannan fannoni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp