Home General NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun...

NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar tsaron Al’umma da adana kadarorin gwamnati wato civil defence ta hannata wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu matasa, lokacin zanga-zangar lumana a nan Kano, ga hukumar sadarwa ta kasa.

Kayan da rundunar ta hannata sun hada da na’ura mai kwakwalwa wato, Computer, Kujeru, Naurar sanyaya daki wato AC da dai sauran kayayyaki na miliyoyin nairori, da rundunar ta kama.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bakin kakakin rundunar shiyyar Kano wato SC Ibrahim Idris Abdullahi.

Idan za a iya tunawa a ranar 10 ga watan Augustan da muke bankwana da shi, wasu matasa sun kutsa kai cikin Sabon ofishin hukumar sadarwa ta kasa dake sakatariyar Audu Bako, inda suka kwashe kayan dake ciki, da sunan zanga-zangar tsadar Rayuwa.

Yanzu haka dai jami’in hukumar sadarwa ta kasa shiyyar Kano ta karbi kayan ta hannun jami’inta wato Aminu Sulaiman Birnin Chido, inda a karshe ya yabawa rundunar tsaron Al’umma ta NSCDC bisa wannan kokari da suka yi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp