Home General NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun...

NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar tsaron Al’umma da adana kadarorin gwamnati wato civil defence ta hannata wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu matasa, lokacin zanga-zangar lumana a nan Kano, ga hukumar sadarwa ta kasa.

Kayan da rundunar ta hannata sun hada da na’ura mai kwakwalwa wato, Computer, Kujeru, Naurar sanyaya daki wato AC da dai sauran kayayyaki na miliyoyin nairori, da rundunar ta kama.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bakin kakakin rundunar shiyyar Kano wato SC Ibrahim Idris Abdullahi.

Idan za a iya tunawa a ranar 10 ga watan Augustan da muke bankwana da shi, wasu matasa sun kutsa kai cikin Sabon ofishin hukumar sadarwa ta kasa dake sakatariyar Audu Bako, inda suka kwashe kayan dake ciki, da sunan zanga-zangar tsadar Rayuwa.

Yanzu haka dai jami’in hukumar sadarwa ta kasa shiyyar Kano ta karbi kayan ta hannun jami’inta wato Aminu Sulaiman Birnin Chido, inda a karshe ya yabawa rundunar tsaron Al’umma ta NSCDC bisa wannan kokari da suka yi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp