Home General NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun...

NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar tsaron Al’umma da adana kadarorin gwamnati wato civil defence ta hannata wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu matasa, lokacin zanga-zangar lumana a nan Kano, ga hukumar sadarwa ta kasa.

Kayan da rundunar ta hannata sun hada da na’ura mai kwakwalwa wato, Computer, Kujeru, Naurar sanyaya daki wato AC da dai sauran kayayyaki na miliyoyin nairori, da rundunar ta kama.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bakin kakakin rundunar shiyyar Kano wato SC Ibrahim Idris Abdullahi.

Idan za a iya tunawa a ranar 10 ga watan Augustan da muke bankwana da shi, wasu matasa sun kutsa kai cikin Sabon ofishin hukumar sadarwa ta kasa dake sakatariyar Audu Bako, inda suka kwashe kayan dake ciki, da sunan zanga-zangar tsadar Rayuwa.

Yanzu haka dai jami’in hukumar sadarwa ta kasa shiyyar Kano ta karbi kayan ta hannun jami’inta wato Aminu Sulaiman Birnin Chido, inda a karshe ya yabawa rundunar tsaron Al’umma ta NSCDC bisa wannan kokari da suka yi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp