Home General NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun...

NSCDC ta mika wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar tsaron Al’umma da adana kadarorin gwamnati wato civil defence ta hannata wasu daga cikin kayan da ta kama a hannun wasu matasa, lokacin zanga-zangar lumana a nan Kano, ga hukumar sadarwa ta kasa.

Kayan da rundunar ta hannata sun hada da na’ura mai kwakwalwa wato, Computer, Kujeru, Naurar sanyaya daki wato AC da dai sauran kayayyaki na miliyoyin nairori, da rundunar ta kama.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bakin kakakin rundunar shiyyar Kano wato SC Ibrahim Idris Abdullahi.

Idan za a iya tunawa a ranar 10 ga watan Augustan da muke bankwana da shi, wasu matasa sun kutsa kai cikin Sabon ofishin hukumar sadarwa ta kasa dake sakatariyar Audu Bako, inda suka kwashe kayan dake ciki, da sunan zanga-zangar tsadar Rayuwa.

Yanzu haka dai jami’in hukumar sadarwa ta kasa shiyyar Kano ta karbi kayan ta hannun jami’inta wato Aminu Sulaiman Birnin Chido, inda a karshe ya yabawa rundunar tsaron Al’umma ta NSCDC bisa wannan kokari da suka yi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp