Home General Nijeriya ta karbi kashin farko na Allurar rigakafin Kyandar biri da Amurka

Nijeriya ta karbi kashin farko na Allurar rigakafin Kyandar biri da Amurka

Sunƙin farko ɗauke da allurar rigakafin cutar ƙyandar biri guda dubu 10 ya isa Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Talata.

Amurka ce dai ta bayar da tallafin allurar rigakafin da kamfanin ƙasar Denmark, Bavarian Nordic ya samar da manufar daƙile nau’in cutar ƙyandar birin ta Clade II, wadda ƙwayar cuta ce da ba ta illa sosai wadda kuma ita ce take yaɗuwa a ƙasar tun shekarar 2017, kamar yadda BBC ta rawaito.

Najeriya dai ta samu mutum fiye da 700 da ake zargin sun kamu da cutar ta kyandar biri inda aka tabbatar da kamuwar mutum 40, duk da cewa ƙwayar cutar da ta kama dukkanninsu ba mai zafi ba ce.

Cutar ta yaɗu zuwa jihohi 13 a Najeriya da suka haɗa da jihohin Bayelsa da Cross River da Ogun da Legas inda nan ne cutar ta fi shafa.

Najeriya ta ce za ta bai wa jami’an lafiya da garuruwan da ke fuskantar haɗarin kamuwa da cutar fifiko wajen allurar rigakafin.

Cibiyar da ke daƙile cutuka masu yaɗuwa a Afirka ta CDD ta yi ƙiyasin cewa ana buƙatar allurar guda miliyan 10 a nahiyar.

Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ce ƙasar da nau’in cutar mai zafi na Clade 1b ya fi yi wa illa a nahiyar.

Tun dai watan Janairun 2023 ne jamhuriyar ta Dimokraɗiyar Congo ta ayyana ɓullar cutar inda mutum dubu 27 suka kamu sannan fiye da 1000 suka mutu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp