Home General Nijeriya ta karbi kashin farko na Allurar rigakafin Kyandar biri da Amurka

Nijeriya ta karbi kashin farko na Allurar rigakafin Kyandar biri da Amurka

Sunƙin farko ɗauke da allurar rigakafin cutar ƙyandar biri guda dubu 10 ya isa Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Talata.

Amurka ce dai ta bayar da tallafin allurar rigakafin da kamfanin ƙasar Denmark, Bavarian Nordic ya samar da manufar daƙile nau’in cutar ƙyandar birin ta Clade II, wadda ƙwayar cuta ce da ba ta illa sosai wadda kuma ita ce take yaɗuwa a ƙasar tun shekarar 2017, kamar yadda BBC ta rawaito.

Najeriya dai ta samu mutum fiye da 700 da ake zargin sun kamu da cutar ta kyandar biri inda aka tabbatar da kamuwar mutum 40, duk da cewa ƙwayar cutar da ta kama dukkanninsu ba mai zafi ba ce.

Cutar ta yaɗu zuwa jihohi 13 a Najeriya da suka haɗa da jihohin Bayelsa da Cross River da Ogun da Legas inda nan ne cutar ta fi shafa.

Najeriya ta ce za ta bai wa jami’an lafiya da garuruwan da ke fuskantar haɗarin kamuwa da cutar fifiko wajen allurar rigakafin.

Cibiyar da ke daƙile cutuka masu yaɗuwa a Afirka ta CDD ta yi ƙiyasin cewa ana buƙatar allurar guda miliyan 10 a nahiyar.

Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ce ƙasar da nau’in cutar mai zafi na Clade 1b ya fi yi wa illa a nahiyar.

Tun dai watan Janairun 2023 ne jamhuriyar ta Dimokraɗiyar Congo ta ayyana ɓullar cutar inda mutum dubu 27 suka kamu sannan fiye da 1000 suka mutu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp