Home General Gwamnan Kano ya bayar da umarnin Rufe Asusun Ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin...

Gwamnan Kano ya bayar da umarnin Rufe Asusun Ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin jihar

Gwamnan ya bayar da umarnin rufe dukkanin asusun ma’aikatu da hukumomin gwamnati domin aiwatar da tsarin asusun bai daya Wanda Zai tabbatar da Sanin Kudade da Suka Shiga da Kuma fita Daga asusun Gwamnatin Jihar Kano

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana haka yayin da yake kaddamar da tsarin tattara kudaden haraji da aiwatar da asusun bai daya ajihar Kano wanda hukumar tattara kudaden haraji ta jiha ta aiwatar.

Gwamna Abba wanda ya nuna damuwarsa kan yadda kudaden harajin jihar Kano suke zirarewa ya ce gwamnatin jiha ta aiwatar da tsarin ne domin dakile hanyoyin zirarewar kudi wanda zai bawa gwamnati damar gudanar da ayyukan raya kasa da cigaban al’uma.

Haka Kuma Gwamnan Ya ja hankalin shugabannin hukumomi da ma’aikatalun jiha dasu yi biyayya ga sabon tsarin, yana Mai jadda cewa gwamnatin jiha zata dauki matakin ladabtarwa ga duk Wanda suka ki yin biyya ga tsarin.

Shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta jiha Dr. Zaid Abubakar Yace abin takaici ne yadda jihohin Lagos da River suka yi wa jihar Kano zarra duk da kasancewar Jihar Kano amatsayin cibiyar kasuwanci a kasar nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp