Home General Ambaliya ta kashe mutum 195 a Najeriya – NEMA

Ambaliya ta kashe mutum 195 a Najeriya – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya (NEMA) ta ce ambaliyar ruwa ta yi sanadiyar mutuwar aƙalla mutum 195 a jihohi 15 na ƙasar a shekarar 2024.

Hukumar ta kuma ce ambaliyar ta raba ƙarin wasu fiye da mutum 208,000 da muhallansu a cikin jihohi 28.

A cikin rahoton da ta fitar kan ƙididdigar ɓarnar da ambaliya ta yi a Najeriya a cikin 2024, NEMA ta ce fiye da kadada 107,000 da gidaje 80,000 ne ambaliyar ta lalata a bana.

Babbar daraktar hukumar NEMA, Hajiya Zubaida Umar, ta shaida wa manema labarai cewa: ‘‘Hasashen yanayi da muka samu daga cibiyar aikin gaggawa da muka kafa a cikin watan Yuli, ya nuna cewa ƙananan hukumomi 140 wannan ambaliya ta shafa, a cikin jihohi 28’’

‘‘Sannan mutum 548,494 ne ambaliyar ta shafa, kuma a cikinsu aƙalla mutum 2,000 ne suka ji rauni sakamakon ambaliyar’’

Hajiya Zubaida Umar ta ƙara da cewa jihohin da ambaliyar ta fi shafa sun haɗa da Bauchi da Zamfara da Sokoto da kuma Jigawa.

‘‘Jihar Bauchi ce ta ɗaya, amma a Jigawa aka fi samun asarar rayuka, amma a Bauchi da Zamfara ne aka fi tafka asarar da ta shafi sauran abubuwa’’

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp