Home General Gwamnatin Najeriya ta yi barazanar riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki

Gwamnatin Najeriya ta yi barazanar riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki

Ma’aikatar lafiyar Najeriya ta bayyana rashin jin daɗinta kan matakin da ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta Najeriya, NARD ta ɗauka na fara yajin aikin gargaɗi na kwana bakwai, duk da ƙoƙarin da gwamnatin ke yi na magance matsalolinsu.

A wata sanarwa da kakakin ma’aikatar, Ado Bako, ya fitar, ya ce gwamnatin ta sanar da aiwatar da dokar “ba aiki, babu albashi” na tsawon kwanakin yajin aikin, ma’ana gwamnati za ta riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki har tsawon kwanakin da suka ɗauka suna yajin aikin, kamar yadda dokar ƙwadago ta tanada.

Bako ya jaddada cewa wannan matakin ba yana nufin yin watsi da halascin damuwar likitocin ba ne amma matakin na da nufin tabbatar da cewa muhimman ayyukan kiwon lafiya sun ci gaba da kasancewa ba tare da samun wata katsewa ba don amfanin jama’a.

Likitocin sun fara yajin aikin ne a ranar Litinin, domin matsa wa gwamnati lamba ta ceto abokiyar aikinsu, Dr Ganiyat Popoola da ke hannun masu garkuwa da mutane tun cikin watan Disambar shekarar da ta gabata.

Bako ya ƙara da cewa, ma’aikatar tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro, sun dukufa wajen ganin an sako Dakta Popoola, kuma a halin da ake ciki, akwai tattaunawa mai ƙarfi da ake yi don ganin a kuɓutar da ita daga hannun masu garkuwa da mutanen.

Ma’aikatar ta buƙaci likitocin da su koma kan teburin tattaunawa, inda ta jaddada muhimmancin samar da haɗin kai da kuma dawwamammen mafita kan ƙalubalen da ke fuskantar fannin kiwon lafiya a Najeriya.

Sanarwar ta sake jaddada aniyar ma’aikatar na yin tattaunawa mai ma’ana tare da yin aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin cimma maslaha mai dorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp