Home General Ambaliya ta kashe mutum 195 a Najeriya – NEMA

Ambaliya ta kashe mutum 195 a Najeriya – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya (NEMA) ta ce ambaliyar ruwa ta yi sanadiyar mutuwar aƙalla mutum 195 a jihohi 15 na ƙasar a shekarar 2024.

Hukumar ta kuma ce ambaliyar ta raba ƙarin wasu fiye da mutum 208,000 da muhallansu a cikin jihohi 28.

A cikin rahoton da ta fitar kan ƙididdigar ɓarnar da ambaliya ta yi a Najeriya a cikin 2024, NEMA ta ce fiye da kadada 107,000 da gidaje 80,000 ne ambaliyar ta lalata a bana.

Babbar daraktar hukumar NEMA, Hajiya Zubaida Umar, ta shaida wa manema labarai cewa: ‘‘Hasashen yanayi da muka samu daga cibiyar aikin gaggawa da muka kafa a cikin watan Yuli, ya nuna cewa ƙananan hukumomi 140 wannan ambaliya ta shafa, a cikin jihohi 28’’

‘‘Sannan mutum 548,494 ne ambaliyar ta shafa, kuma a cikinsu aƙalla mutum 2,000 ne suka ji rauni sakamakon ambaliyar’’

Hajiya Zubaida Umar ta ƙara da cewa jihohin da ambaliyar ta fi shafa sun haɗa da Bauchi da Zamfara da Sokoto da kuma Jigawa.

‘‘Jihar Bauchi ce ta ɗaya, amma a Jigawa aka fi samun asarar rayuka, amma a Bauchi da Zamfara ne aka fi tafka asarar da ta shafi sauran abubuwa’’

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp