Home General Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Zamfara

Al’ummar ƙauyen Matusgi da ke Jihar Zamfara sun kashe ’yan fashin daji 37 biyo bayan wani dauki ba dadi da aka yi a kauyen.

Mazauna ƙauyen Matusgi da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda yunkuro ne a lokacin da ’yan ta’addan suka kai musu hari a ranar Laraba.

Wani wanda abun ya faru a gabansa ya ce  wannan  ab shi ne karon farko da ’yan bindiga suka kwashi kashinnsu a hannun ƙauyen ba.

Ya ce a baya al’ummar ƙauyen sun sha yin fito-na-fito na ’yan fashin daji.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa  ’yan fashin daji sun fara harbul kan mai uwa da wabi daga shigar su kauyen.

Suna cikin harbe-harben ne jama’ar garin suka yi musu kawanya, suka nemi hana su tserewa, suna yi musu luguden wuta, har suka kashe ’yan fashin daji da dama.

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya ce bayan ɗauki-ba-daɗin, mutanen ƙauyukan da ke kusa da su sun ce sun ga ’yan fashin daji suna wucewa da gawarwakin ’yan uwansu a kan babura.

“A wancan har suka fice ne ba yi ba, sai sai bayan da suka tafi suka yi kafin muka san sun shigo mana.”

Ya ce sun buƙaci kuɗin fansa N150,000 a kan kowane mutum guda, amma bayan an biya kuɗin mata bakwai kawai suka sako, har yanzu suna riƙe da sauran

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp