Home General Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Zamfara

Al’ummar ƙauyen Matusgi da ke Jihar Zamfara sun kashe ’yan fashin daji 37 biyo bayan wani dauki ba dadi da aka yi a kauyen.

Mazauna ƙauyen Matusgi da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda yunkuro ne a lokacin da ’yan ta’addan suka kai musu hari a ranar Laraba.

Wani wanda abun ya faru a gabansa ya ce  wannan  ab shi ne karon farko da ’yan bindiga suka kwashi kashinnsu a hannun ƙauyen ba.

Ya ce a baya al’ummar ƙauyen sun sha yin fito-na-fito na ’yan fashin daji.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa  ’yan fashin daji sun fara harbul kan mai uwa da wabi daga shigar su kauyen.

Suna cikin harbe-harben ne jama’ar garin suka yi musu kawanya, suka nemi hana su tserewa, suna yi musu luguden wuta, har suka kashe ’yan fashin daji da dama.

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya ce bayan ɗauki-ba-daɗin, mutanen ƙauyukan da ke kusa da su sun ce sun ga ’yan fashin daji suna wucewa da gawarwakin ’yan uwansu a kan babura.

“A wancan har suka fice ne ba yi ba, sai sai bayan da suka tafi suka yi kafin muka san sun shigo mana.”

Ya ce sun buƙaci kuɗin fansa N150,000 a kan kowane mutum guda, amma bayan an biya kuɗin mata bakwai kawai suka sako, har yanzu suna riƙe da sauran

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp