Home General Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Zamfara

Al’ummar ƙauyen Matusgi da ke Jihar Zamfara sun kashe ’yan fashin daji 37 biyo bayan wani dauki ba dadi da aka yi a kauyen.

Mazauna ƙauyen Matusgi da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda yunkuro ne a lokacin da ’yan ta’addan suka kai musu hari a ranar Laraba.

Wani wanda abun ya faru a gabansa ya ce  wannan  ab shi ne karon farko da ’yan bindiga suka kwashi kashinnsu a hannun ƙauyen ba.

Ya ce a baya al’ummar ƙauyen sun sha yin fito-na-fito na ’yan fashin daji.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa  ’yan fashin daji sun fara harbul kan mai uwa da wabi daga shigar su kauyen.

Suna cikin harbe-harben ne jama’ar garin suka yi musu kawanya, suka nemi hana su tserewa, suna yi musu luguden wuta, har suka kashe ’yan fashin daji da dama.

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya ce bayan ɗauki-ba-daɗin, mutanen ƙauyukan da ke kusa da su sun ce sun ga ’yan fashin daji suna wucewa da gawarwakin ’yan uwansu a kan babura.

“A wancan har suka fice ne ba yi ba, sai sai bayan da suka tafi suka yi kafin muka san sun shigo mana.”

Ya ce sun buƙaci kuɗin fansa N150,000 a kan kowane mutum guda, amma bayan an biya kuɗin mata bakwai kawai suka sako, har yanzu suna riƙe da sauran

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp