Home General Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki

Hukumar kare haƙƙin mai saye ta ƙasa (FCCPC) ta bai wa ‘yan kasuwa a faɗin Najeriya wa’adin wata guda don saukar da farashin kayayyaki da kuma daina tsawwala wa masu saye.

Sanarwar ta fito ne daga bakin sabon mataimakin shugaban hukumar, Mista Tunji Bello, a yayin wani taron kwana ɗaya da masu ruwa da tsaki suka gudanar kan tsawwala farashin kayyayaki a Abuja.

Bello ya jaddada cewa hukumar ta ɗauki matakin ne da nufin magance yawaitar tsadar kayayyaki da ke addabar masu saye a faɗin ƙasar.

Ya yi nuni da cewa, yayin da hukumar ta fahimci ƙalubalen da ‘yan kasuwa ke fuskanta, akwai damuwa kan yadda ƴan kasuwar suka ƙara farashin kayayyaki da gangan da kuma ƙoƙarin haɗa kai tsakaninsu domin cin gajiyar masu saye.

“Akwai gungun ‘yan kasuwa da ke haɗa baki da kai wajen tsawwala wa masu saye” in ji Bello, inda ya buƙaci ƴan kasuwar su yi aiki da kishin ƙasa da adalci.

Hukumar ta FCCPC ta yi amfani da sashe na 155 na dokokin kasuwanci don jaddada muhimmancin matsayar ta a kan farashin riba.

A ƙarƙashin wannan sashe, mutane ko ƙungiyoyin kamfanoni da aka samu da laifin ƙara farashin kayayyaki da gangan za su fuskanci hukunci mai tsanani, gami da tara da kuma ɗauri

Bello ya yi gargadin cewa Hukumar ta shirya tsaf domin ɗaukar tsauraran matakan tsaro a kan wadanda suka keta dokar da zarar wa’adin ya ƙare.

Bello ya bukaci masu ruwa da tsaki da ƴan kasuwa da su ba su haɗin kai, tare da karfafa musu gwiwa kan su rage farashin kayayyakinsu a cikin wata guda.

Hukumar ta FCCPC ta bayyana ƙarara cewa za ta sa ido sosai kan yadda ake bin doka da oda na kasuwanci tare da fara aiwatar da dokar a kan waɗanda ke ci gaba da tsawwala wa masu saye.

Hukumar ta mayar da hankali ne wajen tabbatar da cewa farashin ya yi daidai da kuma yadda kasuwar ke tafiya yadda ya kamata domin kare muradun masu saye da Najeriya gaba ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp