Home General Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki

Hukumar kare haƙƙin mai saye ta ƙasa (FCCPC) ta bai wa ‘yan kasuwa a faɗin Najeriya wa’adin wata guda don saukar da farashin kayayyaki da kuma daina tsawwala wa masu saye.

Sanarwar ta fito ne daga bakin sabon mataimakin shugaban hukumar, Mista Tunji Bello, a yayin wani taron kwana ɗaya da masu ruwa da tsaki suka gudanar kan tsawwala farashin kayyayaki a Abuja.

Bello ya jaddada cewa hukumar ta ɗauki matakin ne da nufin magance yawaitar tsadar kayayyaki da ke addabar masu saye a faɗin ƙasar.

Ya yi nuni da cewa, yayin da hukumar ta fahimci ƙalubalen da ‘yan kasuwa ke fuskanta, akwai damuwa kan yadda ƴan kasuwar suka ƙara farashin kayayyaki da gangan da kuma ƙoƙarin haɗa kai tsakaninsu domin cin gajiyar masu saye.

“Akwai gungun ‘yan kasuwa da ke haɗa baki da kai wajen tsawwala wa masu saye” in ji Bello, inda ya buƙaci ƴan kasuwar su yi aiki da kishin ƙasa da adalci.

Hukumar ta FCCPC ta yi amfani da sashe na 155 na dokokin kasuwanci don jaddada muhimmancin matsayar ta a kan farashin riba.

A ƙarƙashin wannan sashe, mutane ko ƙungiyoyin kamfanoni da aka samu da laifin ƙara farashin kayayyaki da gangan za su fuskanci hukunci mai tsanani, gami da tara da kuma ɗauri

Bello ya yi gargadin cewa Hukumar ta shirya tsaf domin ɗaukar tsauraran matakan tsaro a kan wadanda suka keta dokar da zarar wa’adin ya ƙare.

Bello ya bukaci masu ruwa da tsaki da ƴan kasuwa da su ba su haɗin kai, tare da karfafa musu gwiwa kan su rage farashin kayayyakinsu a cikin wata guda.

Hukumar ta FCCPC ta bayyana ƙarara cewa za ta sa ido sosai kan yadda ake bin doka da oda na kasuwanci tare da fara aiwatar da dokar a kan waɗanda ke ci gaba da tsawwala wa masu saye.

Hukumar ta mayar da hankali ne wajen tabbatar da cewa farashin ya yi daidai da kuma yadda kasuwar ke tafiya yadda ya kamata domin kare muradun masu saye da Najeriya gaba ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp