Home General Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Shugaba Bola Tinubu ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo murnar lashe zaɓe.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ce ta sanar da Okpebholo matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar ranar Asabar 21 ga watan Satumba, inda ya doke sauran ƴan takara.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na X, Tinubu ya yaba wa jagorancin jam’iyyar APC na ƙasa da kuma gwamnonin jam’iyyar bisa jajircewarsu wajen ganin an samu nasara.

Ya buƙaci sabon gwamnan jihar ta Edo da ya ɗauki nasarar a matsayin hakki da aka ɗora masa wajen kai jihar gaba.

“Nasarar ta nuna irin goyon baya da mutane ke yi wa jam’iyyar mu ta APC, ƙoƙari da take yi da kuma tsare-tsare da take ɓullo da su wajen inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Tinubu.

Ya ce Okpebholo ya nuna dattako wajen gayyato ƴan adawa domin a yi tafiya tare da kuma haɗa kan al’ummar jihar don samun ci gaba.

Shugaban Najeriyar ya kuma yaba yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp