Home General Kotu ta dakatar da hukumar VIO daga cin tarar masu ababen hawa...

Kotu ta dakatar da hukumar VIO daga cin tarar masu ababen hawa a Najeriya

Babbar kotun tarayya a Najeriya da ke zamanta a Abuja, ta haramtawa Hukumar Kula da Lafiyar Ababen Hawa ta VIO, ta daina kamawa da kwacewa ko kuma cin tarar masu ababen hawa.

Haka kotun ta umarci jami’an hukumar na VIO su daina tsaida masu ababen hawa akan hanyoyin ƙasar.

Mai shari’a Evelyn Maha ce dai ta yanke wannan hukuncin, bayan da Abubakar Marshal, mai rajin kare hakkin bil’adama ya shigar da ƙara kan lamarin.

A hukuncin nata ta ce, kotun ta gamsu da hujjojin mai ƙara na cewa babu wata doka da ta baiwa waɗanda ake ƙara hurumin tsaidawa da kamawa da kwacewa ko kuma cin tarar masu ababen hawa a kan hanya.

Mai shari’a Maha ta kuma bada umarnin dakatar da waɗanda ake ƙara, daga tauye haƙƙin ƴan Najeriya na yin zirga-zirga yadda suke suke so ba tare da sahalewar doka ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp