Home General Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Wasu da ake zargin ƴan bimdiga sun kashe mutum biyar a wani sabon hari da suka kai karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang shi ya tabbaatr da faruwar hakan a jiya Talata.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa irin harin ya janyo mutuwar mutane biyar bayan kwantan-ɓauna da ƴan bindigar suka yi musu.

“Harin ya yi sanadiyyar rayukan matasa huɗu waɗanda suka fito domin tsare gidajensu. Bayan nan maharan sun kuma kashe wani tsoho bayan yin dirar miƙiya zuwa cikin gidansa,” in ji Fuddang.

Harin dai na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da kai wasu hare-hare, inda aka kashe wasu mutane goma a karamar hukumar ta hanyar yi musu kisan gilla.

Al’ummar yankin sun yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu na fatattakar ƴan bindigar, inda suka yi kira na a ƙara kaimi tare da haɗin gwiwa wajen daƙile irin waɗannan hare-hare a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp