Home General Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Wasu da ake zargin ƴan bimdiga sun kashe mutum biyar a wani sabon hari da suka kai karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang shi ya tabbaatr da faruwar hakan a jiya Talata.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa irin harin ya janyo mutuwar mutane biyar bayan kwantan-ɓauna da ƴan bindigar suka yi musu.

“Harin ya yi sanadiyyar rayukan matasa huɗu waɗanda suka fito domin tsare gidajensu. Bayan nan maharan sun kuma kashe wani tsoho bayan yin dirar miƙiya zuwa cikin gidansa,” in ji Fuddang.

Harin dai na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da kai wasu hare-hare, inda aka kashe wasu mutane goma a karamar hukumar ta hanyar yi musu kisan gilla.

Al’ummar yankin sun yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu na fatattakar ƴan bindigar, inda suka yi kira na a ƙara kaimi tare da haɗin gwiwa wajen daƙile irin waɗannan hare-hare a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp