Home General Taron G20 ya sake fito da damar haɗin kan duniya don kawar...

Taron G20 ya sake fito da damar haɗin kan duniya don kawar da yunwa da talauci – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce tattaunawar da aka yi a taron G20 a Brazil, ta sake bayyana babbar damar haɗin kai tsakanin ƙasashe don tunkarar ƙalubalen da duniya ke fuskanta gaba ɗaya.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinta na Facebook bayan gabatar da jawabi a taron, Shugaba Tinubu ya ce a taron G20 na bana, Najeriya ta amince da yunƙurin shugaban ƙasar Brazil na neman haɗin kan duniya domin kawar da babbar barazanar da duniya ke fuskanta, wato yunwa da talauci.

”Wannan ƙuduri ya yi daidai da muradin Najeriya na yaƙi da yunwa da talauci, da samar da ci gaba mai ɗorewa ta hanyar samar wa ‘yan Najeriya ayyukan yi”, in ji shi.

Shugaban na Najeriya ya sake jaddada shawarar ƙasashen Afirka na sake fasalin cibiyoyin duniya, ciki har da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyar G20, don tabbatar da adalci da tafiya da kowa ta yadda Najeriya da ƙasashen Afirka za su shiga a dama da su wajen ɗaukar matakai a waɗanann cibiyoyi.

”A kan sauye-sauyen tattalin arziki, na jaddada ƙudurin Najeriya na tabbatar da adalci a tsarin haraji na duniya da tsarin hada-hadar kuɗi wanda zai cike giɓin da ke tsakanin manyan da ƙananan ƙasashen duniya”.

Shugaba Tinubu ya kuma a yayin da gwamnatinsa ke neman faɗaɗa haraji ta Najeriya ba tare da ƙara wa ‘yan ƙasa wahala ba, gwamnatin ta mayar da hankali kan rage wahalhalu da ɓullo da ƙarin damarmaki da inganta ayyukan more rayuwa, da ƙarfafa ilimi da cibiyoyin tsaro da zamantakewa, waɗanda ya ce suna da mahimmanci don sake farfaɗo da ci gaban ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp