Home General Hukumar Hisbah a Kano za ta ci gaba da rufe shagunan caca...

Hukumar Hisbah a Kano za ta ci gaba da rufe shagunan caca a jihar

Hukumar Hisbah ta jihar Kano a Najeriya ta ce za ta ci gaba da bin tsarinta na rufe shagunan masu caca bayan hukunci wata kotu.

A ranar Juma’a kotun ƙolin ƙasar ta rushe dokar 2005, da ta amince da kafa hukumar kula da caca tare da halasta cacar wasanni a ƙasar.

Kotun ta ce hukuncin na nufin gwamnatocin jihohi ne ke da wuƙa da nama game da dokokin da suka shafi caca.

Daraktan hukumar Hisbah na jihar Kanon, Dakta Abba Sufi ya ce hukuncin kotun na nufin hukumarsu za ta ci gaba da kai samame tare da rufe shagunan caca a faɗin jihar, saboda haramcin sana’ar a ƙarƙashin dokokin Musulunci.

Abba Sufi ya ce iyayen yara na yawan ƙorafi game da yadda yaransu ke ci gaba da faɗawa komar wannan mummunar sana’a a daidai lokacin da matsin rayuwa da talauci ke ƙaruwa tsakanin al’umma.

Jihar Kano na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya da ake amfani da dokokin addinin Musulunci baya da dokokin ƙasa.

A watan da ya gabata hukumar Hisbar jihar ta kai samame tare da rufe gomman shagunan caca a faɗin birnin Kano.

To sai dai an dakatar da samamen sakamakon ƙarar da wasu ƙungiyoyi suka shigar, dogaro da cewa caca ba laifi ba ne a ƙarƙashin dokokin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp