Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta musanta wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke zarginta da hannu a cikin aikin ƙirƙirar makaman nukiliya a Najeriya.

Daraktan yada labarai na jami’ar, Auwalu Umar, ya bayyana a wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar cewa bidiyon da aka ƙirƙira ta hanyar AI ba gaskiya ba ne, kuma manufarsa ita ce yaudarar jama’a game da shirin makamashin nukiliya a Najeriya.

Ya ce zargin cewa masana na ABU sun taɓa samun kayan aikin ƙirƙirar makami daga cibiyar AQ Khan ta Pakistan ko yin gwajin uranium a Kaduna a shekarun 1980 ba gaskiya bane .

Umar ya ƙara da cewa a lokacin da ake zargin, yawancin masana a cibiyar binciken makamashin nukiliya ta jami’ar (CERT) suna ci gaba da karatu a ƙasashen waje, kuma babu wata shaida da ke nuna an taɓa yin aikin da ya saba wa doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com