Home Labarai Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Kwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ƙaruwar hare-hare da ake samu na baya-bayan nan a ƙasar ya kai matakin da ke buƙatar matakin gaggawa daga hukumomi, musamman daga gwamnatin ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce wajibi ne gwamnatin Najeriya ta sauke babban nauyin da ke kanta na kare rayukan al’umma, ta hanyar ƙarfafa wa jam’ian tsaron ƙasar gwiwa.

”Da farko, sace ɗalibai ƴanmata 25 a Kebbi abin damuwa ne da ke sanya fargabar ko za a maimaita abin da ya faru a baya, sai sacewa da kuma kashe Birgadiya janar M Uba da ƴan ta’adda suka yi a Borno, wanda yana daga cikin lokuta mafi muni a yaƙin da ƙasar ke yi da ta’addanci,” in ji shi.

Ya kuma nuna damuwa game da sace gwamman mutane a Zamfara, da kuma ƙaruwar harin da ƴan bindiga ke kai wa a ƙananan hukumomin Shanono da Ghari a jihar Kano.

”Ina kira a yi gaggawar ceto waɗanda aka sace, domin hare-haren baya-bayan nan na nuna koma baya a yaƙin da ake yi da matsalar tsaro,” a cewar sa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp