Katu ta sami Nnamdi Kanu da laifukan ta’addanci

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta samu jagoran ƙungiyar ƴan aware ta Biafra, Nnamdi Kanu da laifuka bakwai da ake tuhumar sa da aikatawa masu alaƙa da ta’addanci.

Alƙalain da yake shari’ar, Mai Shari’a James Omotosho ya ce masu gabatar da ƙarar sun tabbatar da tuhume-tuhumen da ake yi wa Nanamdi Kanu.

Tuhume-tuhumen da ake yi wa Kanu sun haɗa da ta’addanci da tunzura jama’a su kashe ƴan sanda da kasancewa mamba a haramtacciyar ƙungiyar IPOB da gwamnatin Najeriya ta haramta da kuma yaɗa farfagandar ta’addanci.

Mai Shari’a Omotosho ya ɗage zaman na wani ɗan lokaci inda ya ce zai yanke wa Nnamdi Kanu hukunci idan aka koma nan ba da jimawa ba.

Ana sa ran wannan ya kawo ƙarshen kimanin shekara 10 da aka kwashe ana shari’a, tun bayan da gwamnati ta gurfanar da shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com