Home Labarai Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnan Kano ya magantu ka matsalar tsaro a jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatarwa mazauna jihar cewa al’amuran tsaro suna tafiya yadda ya kamata, kuma babu wata barazana da ya kamata ta tayar da hankalin jama’a.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya PRNigeria a safiyar litinin.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya bayar da tabbacin ne bayan taron majalisar tsaron jihar da aka yi a ranar Lahadi tare da manyan jami’an tsaro, inda aka sake jaddada kudurin gwamnati na tabbatar da zaman lafiya a dukkan yankunan jihar.

Gwamnatin ta ce duk wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta na cewa akwai gagarumar barazanar tsaro a Kano, ba shi da tushe balle makama. Ta ce babu wani sahihin bayanan asiri da ke nuna akwai matsalar tsaro da ta taso ko ta gabatowa a jihar .

Sanarwar ta jaddada cewa gwamnati ba za ta lamunci yada bayanan ƙarya da nufin tayar da hankalin jama’a ba, tare da gargadin cewa irin wannan ɗabi’a na iya janyo hukunci daga hukumomi.

Gwamnatin ta bayyana cewa tana aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, tare da tabbatar da cewa jami’an tsaro sun kasance cikin shiri, kuma an tura su muhimman wurare, suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da zaman lafiya a Kano .

Sanarwar ta kara da cewa an sanya dukkan sassan Kano cikin tsauraran matakan sa ido, tare da ingantaccen tsarin tsaro da ke aiki yadda ya kamata.

Gwamnatin ta roki jama’a su kwantar da hankalinsu, su guji yada jita-jita a kafafen sada zumunta. Ta kuma yi gargaɗin cewa masu yada labaran ƙarya su daina, domin hakan na iya jawo wa mai yi hukunci.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa gwamnati na kara inganta ayyukan leken asiri, haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, da kuma sabunta dabarun tsaro na zamani a fadin jihar Kano

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp